HausaTv:
2025-06-15@19:52:24 GMT

Kasashen Saudiyya Da Iran Sun Ki Amincewa Da Shirin Korar Falasdinawa Daga  Kasarsu

Published: 11th, February 2025 GMT

Da marecen jiya Litinin ne aka yi tattaunawa ta wayar tarho a tsakin ministocin harkokin wajen Iran da na Saudiyya akan shirin Donald Trump na korar Falsdinawa daga Gaza,inda kasashen biyu su ka ki amincewa da shi.

Ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci, da takwaransa na Saudiyya Faysal Bin Farhaan, sun nuna kin amincewarsu da shirin na shugaban kasar Amurka akan mutanen Gaza.

Ministan harkokin wajen Saudiyya Faysal Bin Farhan ya ce, Saudiyya tana da matsaya tabbatacciya da ita ce kin amincewa da duk wani shiri na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza zuwa wata kasa.”

Ministan na Saudiyya ya nuna goyon bayansa ga kiran da Iran ta yi na yin taron kungiyar kasashen musulmi domin tattaunawa wannan batu.

A nashi gefen ministan harkokin wajen Iran ya ce; Shirin na Donald Trump na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza, ci gaba ne na tsohon shirin ‘yan mulkin mallaka na shafe hakkokin Falasdianwa, tare da yin kira da a dauki matakin fuskantar wannan makarkashiya.

Haka nan kuma minstan harkokin wajen na Iran ya yi tir da furucin Benjemin Netanyahu dake cewa a kafa kasar Falasdinu a cikin Saudiyya, tare da cewa wannan Magana ce ta dagawa da girman kai na ‘yan mamaya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Bisa la’akari da haka, a fili kasar Sin tana adawa da matakin da Isra’ila ta dauka na keta dokokin kasa da kasa, inda ta kai wa kasar Iran hari, lamarin da ba za a amince da shi ba, musamman ma ta la’akari da yadda kasashe daban daban ke ci gaba da neman hanyar daidaita batun nukiliyar kasar ta Iran ta hanyar siyasa.

Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin ta bukaci Isra’ila da Iran da su warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, da lalubo bakin zaren kasancewa tare cikin kwanciyar hankali da lumana. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje