Kasashen Saudiyya Da Iran Sun Ki Amincewa Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Kasarsu
Published: 11th, February 2025 GMT
Da marecen jiya Litinin ne aka yi tattaunawa ta wayar tarho a tsakin ministocin harkokin wajen Iran da na Saudiyya akan shirin Donald Trump na korar Falsdinawa daga Gaza,inda kasashen biyu su ka ki amincewa da shi.
Ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci, da takwaransa na Saudiyya Faysal Bin Farhaan, sun nuna kin amincewarsu da shirin na shugaban kasar Amurka akan mutanen Gaza.
Ministan harkokin wajen Saudiyya Faysal Bin Farhan ya ce, Saudiyya tana da matsaya tabbatacciya da ita ce kin amincewa da duk wani shiri na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza zuwa wata kasa.”
Ministan na Saudiyya ya nuna goyon bayansa ga kiran da Iran ta yi na yin taron kungiyar kasashen musulmi domin tattaunawa wannan batu.
A nashi gefen ministan harkokin wajen Iran ya ce; Shirin na Donald Trump na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza, ci gaba ne na tsohon shirin ‘yan mulkin mallaka na shafe hakkokin Falasdianwa, tare da yin kira da a dauki matakin fuskantar wannan makarkashiya.
Haka nan kuma minstan harkokin wajen na Iran ya yi tir da furucin Benjemin Netanyahu dake cewa a kafa kasar Falasdinu a cikin Saudiyya, tare da cewa wannan Magana ce ta dagawa da girman kai na ‘yan mamaya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
Ya ce Sin tana maraba da kamfanonin dake fuskantar kalubale su tuntubi ma’aikatar ko hukumomi masu ruwa da tsaki, yana cewa, ma’aikatar za ta nazarci ainihin abubuwan dake faruwa da kuma bayar da damar fitar da kayayyaki ga wadanda suka cancanta. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA