‘Nijeriya ce ƙasa ta 140 mafi rashawa a Duniya’
Published: 11th, February 2025 GMT
Nijeriya ta zama ƙasa ta 140 a cikin jerin ƙasashen da aka fi tafka cin hanci da rashawa a duniya a shekarar 2024 a cewar ƙungiyar Transparency International.
A cikin rahoton wanda ta fitar a yau, Transparency ta ce Denmark ce ƙasar da ta kasance wadda ba ta fuskantar matsalar ta cin hanci da rashawa.
Alƙaluman ƙasashe mafi cin hanci da rashawa a duniya ya nuna yadda Nijeriya ta koma matsayin ta 140 daga ta 145 da take a baya a sahun ƙasashe 180 mafiya cin hanci da rashawa a duniya
Rahoton wanda ya yi nazari kan ƙasashen ya yi amfani da masana da ’yan kasuwa wajen tantance matsayin kowace ƙasa.
Ma’aunin tantance munin cin hancin ya kama ne daga maki sifili zuwa 100, inda sifili ke nufin mummunan matsalar cin hanci yayin da 100 ke nufin rashin matsalar baki ɗaya.
Rahoton ya yi la’akari ne da ƙarfin hukumomi a ƙasashen, da inganci zaɓe da kuma ɗabi’ar gwamnati.
Transparency International ta ce Nijeriya tare da wasu ƙasashe kamar Uganda, Mexico, Madagascar, Iraq da Kamaru sun samu maki 26 ne cikin 100.
Sudan ta Kudu da Somaliya da kuma Venezuela na cikin ƙasashen da aka fi tafka rashawa a duniya.
Transparency ta ce cin hanci babban barazana ce ga sauyin yanayi. Ta ce hakan yana kawo cikas wajen batun rage fitar da gurɓataccen iska da masana’antu ke yi.
Shugaban ƙungiyar François Valérian ya bayyana cin hanci da rashawa a matsayin mummunar matsala mai haɗarin gaske ga duniya.
Ya ce, duk da cewa wasu ƙasashe sun yi hoɓɓasa wajen murmurewa daga matsalolin na cin hanci da Rashawa amma har yanzu wasu na cigaba da ganin ta’azzarar matsalar.
Ƙungiyar ta ce daga shekarar 2012 akwai ƙasashe 32 cikin 180 da suka yi ƙoƙarin rage matsalar ta cin hanci da rashawa kodayake 148 daga ciki ko dai suna inda suke ko kuma matsalar ta ta’azzara.
Transparency International ta ce har yanzu ƙasashe 43 basu sauya daga matakin da suke tsawon shekaru ba.
A cewar ƙungiyar, akwai biliyoyin mutane da ke rayuwa a ƙasashen da rashawa ke ci gaba da illata rayukan jama’a a wani yanayi da take haƙƙin ɗan adam ke kaiwa ƙololuwa a irin ƙasashen.
François Valérian ya buƙaci ƙasashe su miƙe tsaye wajen yaƙar matsalar ta rashawa wadda ya ce babbar barazana ce ga ci gaban demokraɗiyya da taɓarɓarewar tsaro baya ga ta’azzara take haƙƙin ɗan adam.
A shekarar 2019 Nijeriya ta koma ta 146 bayan samun maki 26 yayinda ta koma ta 154 a 2021 bayan samun maki 24, inda ta koma ta 145 a 2023 bayan samun maki 25 gabanin komawa ta 140 a bana bayan samun maki 26.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: rashawa Transparency International cin hanci da rashawa a rashawa a duniya bayan samun maki Nijeriya ta matsalar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
Tawagar Iran ta fice daga taron majalisun dokokin kasashen duniya kafin fara jawabin jami’in gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila a zaman taron
A wata gagarumar nuna rashin amincewa da tushen zaluncin da ya addabi duniya, tawagogin kasashen Iran, Yemen, da Falasdinu sun fice daga zaman taron Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, bayan da shugaban majalisar dokokin Isra’ila “Knesset” zai fara gabatar da jawabinsa mai kunshe da bayanai neman tunzura jama’a, wanda kuma bayanai suka haifar da cece-kuce a tsakanin wadanda suka zauna suka saurara.
A cikin jawabin shugaban majalisar dokokin Isra’ila “Knesset” ya bayyana cewa; Akwai yiwuwar samar da ‘yantacciyar kasar Falasdinu a wajen yankunan Falasdinu, musamman a biranen London da Paris na kasashen Birtaniya da Faransa.
Wannan matakin na nuna rashin amincewa da yadda yahudawan sahayoniyya suke adawa tare da yin watsi da hakikanin samuwar Falasdinawa da kuma kokarin tauyaye hakkin al’ummar Falasdinu.
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibaf ne ya jagoranci tawagar ‘yan majalisun dokokin kasar Iran zuwa wajen taron da ya hada shugabannin majalisun dokokin duniya karo na shida a birnin Geneva na kasar Switzerland.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci