Aminiya:
2025-05-01@06:21:23 GMT

Nijeriya ce ƙasa ta 140 mafi rashawa a Duniya — CPI

Published: 11th, February 2025 GMT

Nijeriya ta zama ƙasa ta 140 a cikin jerin ƙasashen da aka fi tafka cin hanci da rashawa a duniya a shekarar 2024 a cewar ƙungiyar Transparency International.

A cikin rahoton wanda ta fitar a yau, Transparency ta ce Denmark ce ƙasar da ta kasance wadda ba ta fuskantar matsalar ta cin hanci da rashawa.

BUA ya raba wa asibitoci magunguna a Sakkwato Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya suya sheka daga PDP zuwa APC

Alƙaluman ƙasashe mafi cin hanci da rashawa a duniya ya nuna yadda Nijeriya ta koma matsayin ta 140 daga ta 145 da take a baya a sahun ƙasashe 180 mafiya cin hanci da rashawa a duniya

Rahoton wanda ya yi nazari kan ƙasashen ya yi amfani da masana da ’yan kasuwa wajen tantance matsayin kowace ƙasa.

Ma’aunin tantance munin cin hancin ya kama ne daga maki sifili zuwa 100, inda sifili ke nufin mummunan matsalar cin hanci yayin da 100 ke nufin rashin matsalar baki ɗaya.

Rahoton ya yi la’akari ne da ƙarfin hukumomi a ƙasashen, da inganci zaɓe da kuma ɗabi’ar gwamnati.

Transparency International ta ce Nijeriya tare da wasu ƙasashe kamar Uganda, Mexico, Madagascar, Iraq da Kamaru sun samu maki 26 ne cikin 100.

Sudan ta Kudu da Somaliya da kuma Venezuela na cikin ƙasashen da aka fi tafka rashawa a duniya.

Transparency ta ce cin hanci babban barazana ce ga sauyin yanayi. Ta ce hakan yana kawo cikas wajen batun rage fitar da gurɓataccen iska da masana’antu ke yi.

Shugaban ƙungiyar François Valérian ya bayyana cin hanci da rashawa a matsayin mummunar matsala mai haɗarin gaske ga duniya.

Ya ce, duk da cewa wasu ƙasashe sun yi hoɓɓasa wajen murmurewa daga matsalolin na cin hanci da Rashawa amma har yanzu wasu na cigaba da ganin ta’azzarar matsalar.

Ƙungiyar ta ce daga shekarar 2012 akwai ƙasashe 32 cikin 180 da suka yi ƙoƙarin rage matsalar ta cin hanci da rashawa kodayake 148 daga ciki ko dai suna inda suke ko kuma matsalar ta ta’azzara.

Transparency International ta ce har yanzu ƙasashe 43 basu sauya daga matakin da suke tsawon shekaru ba.

A cewar ƙungiyar, akwai biliyoyin mutane da ke rayuwa a ƙasashen da rashawa ke ci gaba da illata rayukan jama’a a wani yanayi da take haƙƙin ɗan adam ke kaiwa ƙololuwa a irin ƙasashen.

François Valérian ya buƙaci ƙasashe su miƙe tsaye wajen yaƙar matsalar ta rashawa wadda ya ce babbar barazana ce ga ci gaban demokraɗiyya da taɓarɓarewar tsaro baya ga ta’azzara take haƙƙin ɗan adam.

A shekarar 2019 Nijeriya ta koma ta 146 bayan samun maki 26 yayinda ta koma ta 154 a 2021 bayan samun maki 24, inda ta koma ta 145 a 2023 bayan samun maki 25 gabanin komawa ta 140 a bana bayan samun maki 26.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: rashawa Transparency International cin hanci da rashawa a rashawa a duniya bayan samun maki Nijeriya ta matsalar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

“Lokacin da abubuwa suka fara lalacewa a lokacin shugaba Buhari, na fito na faɗi gaskiya. Lokacin da tsarin sauya fasalin Naira ya jefa jama’a cikin wahala, na ƙalubalanci gwamnati duk da cewa jam’iyyar APC ce ke kan mulki. Na fi biyayya ga Nijeriya fiye da kowane mutum,” in ji shi.

El-Rufai ya ƙaryata jita-jitar cewa fushinsa da gwamnatin Shugaba Tinubu ne ya sa ya fice daga APC.

Ya ce yana da shekaru 65, kuma babu wani abu da ya rage masa a siyasa da zai nema, sai dai kawai yana jin cewa matsalolin Nijeriya sun yi tsanani sosai wanda ba zai zauna ya yu shiru ba.

“Zan iya yin ritaya cikin kwanciyar hankali, amma Nijeriya na fuskantar babbar barazana. Wannan ba don kaina ba ne – don ceton ƙasa ne,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa dole a zaɓi shugaban ƙasa mai nagarta da hangen nesa, ba wai kawai din ya fito daga wata jiha ba.

“Matsalolin da muke fuskanta sun fi girman la’akari da inda mutum ya fito. Muna buƙatar shugabanni masu hangen nesa da ƙwarewa don gyara Nijeriya,” ya bayyana.

Da yake magana kan sauya sheƙar wasu ‘yan siyasa zuwa APC, El-Rufai ya ce jam’iyyar SDP tana mayar da hankali ne kan gina goyon baya daga jama’a, ba wai kawai neman manyan ‘yan siyasa ba.

“Gwamna ɗaya yana da ƙuri’a ɗaya ne kawai. Jama’a ne ke yin zaɓe, ba manyan ‘yan siyasa ba,” ya jaddada.

A ƙarshe, El-Rufai ya ce tafiyar SDP tana ci gaba da karɓuwa a dukkanin sassan Nijeriya, ba a yankuna kaɗan kaɗai ba.

“Muna ci gaba da gina goyon baya a faɗin ƙasar nan. Aikin gina ƙasa yana faruwa ne a tsakanin talakawa, ba kawai a kafafen yaɗa labarai ba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara