Aminiya:
2025-05-01@04:39:59 GMT

Dalilin da na ziyarci Obasanjo — Atiku

Published: 10th, February 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya bayyana dalilin ziyarar da ya kai wa tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a wannan Litinin ɗin.

Aminiya ta ruwaito cewa, da misalin ƙarfe 12:36 na yau Litinin ce tawagar da Atikun ya jagoranta ta isa gidan tsohon Shugaban Ƙasar da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya samu rakiyar tsohon gwamnan Jihar Kuros Riba, Liyel Imoke da takwaransa na Sakkwato, Sanata Aminu Tambuwal haɗi da ɗan Majalisar Dattawa mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya, Sanata Abdul Ningi.

Bayanai sun ce an shafe tsawon sa’a ɗaya da rabi ana ganawar wadda aka yi ta a bayan labule.

Sai dai da yake zantawa da manema labarai da misalin ƙarfe 2:11, Atiku ya bayyana cewa ziyarar ban girma ce kawai ta kawo shi wurin ubangidan nasa.

Haka kuma duk da tsananta ƙwaƙƙwafi da manema labaran suka yi, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar ya ce ba zai ce uffan ba dangane da duk wani batu da ya shafi siyasa.

“Ziyarar ban girma ce ta kawo ni saboda haka ba zan ce komai a kan abin da ya shafi siyasa ba,” in ji Atiku.

Atiku ya kasance mataimaki ga Obasanjo daga watan Mayun 1997 zuwa Mayun 2007.

A bayan nan dai Atiku wanda ke muradin kujerar Shugaban Nijeriya ya yi ganawa daban-daban kan abin da ake zargin shirye-shiryen tunkarar Zaɓen 2027.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar Zaɓen 2027 ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno

Wasu abubuwan fashewa da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram ne suka dasa, sun kashe kimanin mutane 26, ciki har da mata da ƙananan yara a kusa da garin Rann da ke Ƙaramar Hukumar Kala Balge ta Jihar Borno.

Majiyoyin tsaro da na cikin gari sun bayyana cewa mutane da dama sun jikkata bayan da motar da ke ɗauke da wadanda abin ya shafa zuwa Gambarou Ngala ta taka abin fashewar.

Wata majiya ta ce, “Ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma rahotanni na farko sun nuna cewa mata huɗu da yara shida da maza 16 ne suka mutu a wannan fashewar.”

Ta ci gaba da cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Furunduma, kimanin kilomita 11 daga garin Rann, da misalin karfe 11 na safe a ranar Litinin.

Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya

Ta ƙara da cewa an kai wasu da suka jikkata asibitin Rann domin kula da su.

Babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren sojoji ko ’yan sanda game da faruwar lamarin.

Sai dai kuma, kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, Kenneth Daso, bai yiwu ba saboda layin wayarsa ba ya shiga.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Xi Jinping Ya Ziyarci Sabon Bankin Raya Kasashen BRICS
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”