Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari
Published: 9th, February 2025 GMT
Tsohon Kwamishinan Zaɓe na Jihar Adamawa, Hudu Ari, ya ce bai damu da korar da aka yi masa ba, amma yana nan a kan bakansa cewa Aisha Binani ta jam’iyyar APC ce, ta lashe zaɓen gwamna na 2023.
An dakatar da Hudu Ari bayan da ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen tun kafin a kammala tattara sakamakon ƙuri’u.
Sai dai ya ce yana da hujjojin da ke nuna cewa Binani ta doke Gwamna Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP.
Da yake magana da manema labarai a Bauchi, Ari ya rantse da Alƙur’ani mai girma cewa manyan jami’an zaɓe sun yi watsi da hujjojinsa kan maguɗin zaɓe.
Ya zargi shugaban sashen Kimiyya da Fasaha na INEC a Adamawa da yin aringizon ƙuri’u, sannan jami’an tsaro sun kama wasu jami’an gwamnati suna canza sakamakon zaɓe.
Ari ya kuma zargi shugaban INEC da kotun zaɓe da yin watsi da bayanansa.
Ya ce ba a ba shi damar kare kansa ba, ko kuma tuntuɓar iyalansa domin yanke shawarar ɗaukar matakin shari’a.
Ya ce bai damu da korarsa daga aiki da aka yi ba, illa ɓata masa suna da aka yi a kafafen yaɗa labarai.
Ya ƙara da cewa rayuwarsa ta shiga hatsari yayin da ake gudanar da zaɓe, inda ya bayyana yadda shi da wasu jami’an zaɓe aka yi musu barazana don su ayyana gwamna mai ci a matsayin wanda ya lashe zaɓen jihar.
A cewarsa, an janye masa tsaro bayan ya ƙi amincewa da buƙatar.
Duk da cire shi daga muƙaminsa, Ari ya dage kan cewar ya bi dokokin zaɓe kuma ya yi abin da ya dace.
Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su kasance masu gaskiya da adalci a lokacin zaɓe, tare da gargaɗin cewa rashin yin hakan zai iya jefa dimokuraɗiyya cikin wani hali.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hudu Ari Maguɗin Zaɓe Zaɓen
এছাড়াও পড়ুন:
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
“Ya zamar mana wajbi, mu kulla wannan hadakar, musamman domoin mu tabbatar da cewa, mun tsaftace tsarin,” Inji Dantsoho.
Ya kara da cewa, wannan aikin, ba wai kawai za kara habaka samar da kariya da kuma kara ingnata tsaro bane, har da kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara ciyar da tattalin arzikin kasar nan gaba.
A cewar Shugaban, cunkoson da ake samu a Tashar ta Tin Can Island na ci gaba da haifar da jinkiri da rashin gudanar da ayyuka yadda suka kamata da kuma rage gudanar da hada-hadar kasuwanci, yadda ta kamata, wanda kuma hakan, ke janyowa kara habaka tattalin arzikin kasar.
Dantsoho wanda Babban Janar Manaja na sashen kula da tsaro a Hukumar ta NPA Mista Anthony Edosomwan ya wakilce shi a wajen kaddamar da aikin ya bayyana cewa, za a gudanar da aikin ne, zuwa kwana uku, musamman domin a samu nasarar gudanar da aikin.
Shugaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ya wallafa a kafafen yada labarai, kan sanarwar wayar da kan jama’a kan batun mahimmancin, tsaftace Tashar ta Tin Can Island.
“Wannan wani mataki ne, da aka samu goyon bayan masu ruwa da tsaki ciki har da masu yin amfani da Tashar da ‘yan kasuwa da kuma sauran alummar da ke a kusa da yankin”, A cewar Dantsoho.
Shugaban ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA ba za ta yi kasa a guiwa, wajen kara mayar da hankali da kuma zagewa, domin ta samu cin nasara wajen tabbatar da tsaftace muhalli da kuma samar da kyakyawan yanayi, a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ba.
“Yanayi na samun gurbatacciyar Iska da kutsen da ake yiwa Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, abu ne da Hukumar ta NPA, ba za ta rungume hannu ta bari ba, ” Inji Dantsoho.
“Wannan aikin na tsafrace Tashar ba wai kawai na da alfanu ga ayyukan da ake gudanarwa a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar bane, hatta alumomin da suke daura da Tashoshin, suma zai yi masu alfanu,“ A cewar Shuaban .
Shuaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ta NPA da faro shi a wannan shekarar ta 2025, na daga cikin shiryae-shiryen rage cunkoso da kuma samar da saukin gudanar da ayyuka, Hukumar ta NPA, wanda hakan zai taimaka matuka wajen samar da kyakywar makoma ga Tashoshin Jiragen Ruwa, da ke a daukacin kasar nan.
A cewar Shugaban, wannan hadakar da sauran jami’an tsaro da kuma yin gangamin na wayar da kan alumma, Hukumar na bukatar goyon bayan alumma, dominn ta samu nasarar, aikin da ta sanya a gaba,
“A saboda haka, Mahukuntan Hukumar ta NPA, na bukatar goyon baya da hadin kan jama’a musamman domin a samar da kyakyawan yanin da ya dace a Tashar Jirgin Ruwan,” A cewar Shugaban.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp