Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari
Published: 9th, February 2025 GMT
Tsohon Kwamishinan Zaɓe na Jihar Adamawa, Hudu Ari, ya ce bai damu da korar da aka yi masa ba, amma yana nan a kan bakansa cewa Aisha Binani ta jam’iyyar APC ce, ta lashe zaɓen gwamna na 2023.
An dakatar da Hudu Ari bayan da ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen tun kafin a kammala tattara sakamakon ƙuri’u.
Sai dai ya ce yana da hujjojin da ke nuna cewa Binani ta doke Gwamna Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP.
Da yake magana da manema labarai a Bauchi, Ari ya rantse da Alƙur’ani mai girma cewa manyan jami’an zaɓe sun yi watsi da hujjojinsa kan maguɗin zaɓe.
Ya zargi shugaban sashen Kimiyya da Fasaha na INEC a Adamawa da yin aringizon ƙuri’u, sannan jami’an tsaro sun kama wasu jami’an gwamnati suna canza sakamakon zaɓe.
Ari ya kuma zargi shugaban INEC da kotun zaɓe da yin watsi da bayanansa.
Ya ce ba a ba shi damar kare kansa ba, ko kuma tuntuɓar iyalansa domin yanke shawarar ɗaukar matakin shari’a.
Ya ce bai damu da korarsa daga aiki da aka yi ba, illa ɓata masa suna da aka yi a kafafen yaɗa labarai.
Ya ƙara da cewa rayuwarsa ta shiga hatsari yayin da ake gudanar da zaɓe, inda ya bayyana yadda shi da wasu jami’an zaɓe aka yi musu barazana don su ayyana gwamna mai ci a matsayin wanda ya lashe zaɓen jihar.
A cewarsa, an janye masa tsaro bayan ya ƙi amincewa da buƙatar.
Duk da cire shi daga muƙaminsa, Ari ya dage kan cewar ya bi dokokin zaɓe kuma ya yi abin da ya dace.
Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su kasance masu gaskiya da adalci a lokacin zaɓe, tare da gargaɗin cewa rashin yin hakan zai iya jefa dimokuraɗiyya cikin wani hali.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hudu Ari Maguɗin Zaɓe Zaɓen
এছাড়াও পড়ুন:
PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
– Emmanuel Adegbola Aina – AIG na wucin gadi, sashen leƙen asiri
– Omolara Ibidun Oloruntola
– Hassan Abdu Yababet – CP, Kwalejin ‘Yan Sanda Jos
– Bretet Emmanuel Simon – CP Jihar Taraba
– Enyinnaya Inonachi Adiogu – CP, FCID, Gombe
– Aminu Baba Raji – CP, FCID Alagbon
– Mohammed Mu’azu Usman – CP, Tashoshin Gabas, P/Harcourt
– Festus Chinedu Oko – AIG na wucin gadi, sashen DLS, Hedkwatar
– Ronke Nurat Okunade – CP, SFU FCID Annex, Lagos
Kazalika, PSC ta amince da:
– Ɗaga darajar DCP 16 zuwa CP
– Ɗaga darajar ACP 27* zuwa DCP
– Ɗaga CSP 145 zuwa ACP, ciki har da likitoci, ma’aikatan lafiya, injiniyoyi na jiragen sama, da limamai
– Ɗaga SP 29 (na musamman na sashen kimiyyar sadarwa da aikace-aikace da AFIS) zuwa CSP
– Ɗaga DSP 38 zuwa SP
Wani ACP ɗaya bai samu damar halarta ba, don haka ba a ɗaga darajarsa ba.
Sabbin CP 16 sun haɗa da:
– Uduak Otu Ita
– Sheikh Mohammed Danko
– Charles Ezekwesiri Dike
– Nnana Oji Ama (FCID Intelligence)
– Gabriel Onyilo Eliagwu
– Abiola Reuben Olutunde
– Yakubu Useni Dankaro
– Michael Adegoroye Falade
– Aina Adesola
– Umar Ahmed Chuso
– Emefile Tony Osifo
– Innocent Ilogbunam Anagbado
– Musa Mohammed Sani
– Victor Avwerosuo Erivwode (DC SEB, FCID)
– Omoikhudu Philip
– Sylvester Edogbanya
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp