‘Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa
Published: 9th, February 2025 GMT
Ga wasu manyan ‘yan kwallo da tauraronsu ke haskawa a duniya, wadanda asalin ‘yan Nijeriya ne, wato ko dai iyayensu baki daya ko wani daga cikin iyayen ‘yan Nijeriya ne.
Jamal Musiala (Jamus)
Matashin dan wasa Jamal Musiala, wanda aka haifa a ranar 26 ga Fabrairun shekarar 2003, fitaccen dan kwallon kasar Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich ta Jamus din kuma yana cikin matasan ‘yan kwallon da suke tashe a duniya a yanzu saboda ba za ka lissafa matasan ‘yan wasa guda biyar ba a duniya ba tare da ka saka sunansa ba.
Matashi Musiala ya wakilci kasar Ingila a kwallon matakin yara, kafin ya koma Jamus da buga wasa sannan kuma ya lashe kofuna da dama irin su gasar Bundesliga guda hudu da sauran kofuna, sannan ya samu kyaututtuka da dama tun daga lokacin da kungiyar Bayer Munchen ta fara saka shi a wasa tun yana dan shekara 17 a duniya.
Karim Adeyemi
Karim-Dabid Adeyemi wanda aka haifa a ranar 18 ga watan Janairun shekarar 2002, dan wasan Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Borussia Dortmund. An haifi dan wasan a birnin Munich, wanda mahaifinsa asalin dan Nijeriya ne, amma mahaifiyarsa ‘yar Romaniya ne kuma a kwanakin baya danwasan da ke buga wasa a Dortmund da ke Jamus ya kusa komawa kungiyar kwallon kafa ta Napoli ta kasar Italiya kafin daga baya cinikin ya rushe bayan yaki amincewa da tafiya.
A baya-bayan nan Karim Adeyemi ya bude wata gidauniya a Nijeriya kuma ya bude gidauniyar ne a birnin Ibadan da ke Jiyar Oyo a kudu maso yammacin kasar nan, inda ya ce gidauniyar za ta mayar da hankali kan koyar da wasanni da ilimi, sannan a lokacin da ya ziyarci Nijeriya, Adeyemi ya shaida wa manema labarai cewa nan gaba yana tunanin komawa buga wasa a gasar Premier ta Ingila.
Michael Olise
Shima matashin dan wasan an haife shi ne a ranar 12 ga Disamban 2001, dan kwallo da a yanzu yake wakiltar Faransa kuma yake buga wasa a kungiyar Bayern Munich ta kasar Jamus. Olise wanda ya koma Jamus da buga wasa daga kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace asalin mahaifinsa dan Nijeriya ne, amma mahaifiyarsa ‘yar Aljeriya ce mazauniyar Faransa. Kuma yanzu haka yana daya daga cikin matasan ‘yan wasan da tauraruwarsu take haskawa a nahiyar Turai.
Noni Madueke
Shi dai asalin sunansa shi ne Chukwunonso Tristan “Noni” Madueke, kuma an haife shi ne a ranar 10 ga Maris a shekarar 2002 kuma yanzu yana wakiltar kasar Ingila ne, sannan yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta Ingila kuma shima asalin mahaifinsa dan Nijeriya, amma shi a Ingila aka haife shi, sannan itama mahaifiyarsa ‘yar asalin kasar Ingila ce.
Bukayo Saka
Bukayo Saka fitaccen dan kwallo ne da a yanzu yake jan zarensa a kungiyar kwallon kafa ta Arsenal da ke Ingila kuma danwasan wanda asalin sunansa Bukayo Ayoyinka Temidayo Saka, iyayensa Adenike da Yomi Saka duka ‘yan Nijeriya ne kuma a baya ya sha bayyana cewa yana alfahari da kasancewarsa dan Nijeriya, kuma ya kan ziyarci kasar nan a wasu lokutan.
Ethan Chidiebere Nwaneri
Ethan Chidiebere Nwaneri wanda aka haifa a ranar 21 ga watan Maris na 2007, matashin danwasa ne da a yanzu yake tashe a kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, kuma an haife shi ne a arewacin Landan, amma iyayensa ‘yan Nijeriya ne, sannan ya wakilci tawagar ‘yanwasan kasa da shekara 16 da 17 da 19 sai dai har yanzu ba wakilci babbar tawagar Ingila ba, wanda hakan ya sa za a iya gayyatarsa Nijeriya.
Joshua Orobosa Zirkzee
Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Bologna dake kasar Italiya, Joshua Orobosa Zirkzee wanda aka haifa a ranar 22 ga Mayun 2001, dan kwallo ne da yake wakiltar kasar Netherlands, kuma yake buga wasa a yanzu a kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta Ingila sanann an haife shi ne a birnin Schiedam, sai dai shi mahaifiyarsa ce ‘yar Nijeriya, amma mahaifinsa dan Netherland ne.
কীওয়ার্ড: a kungiyar kwallon kafa ta wanda aka haifa a ranar yan Nijeriya ne dan Nijeriya buga wasa a
এছাড়াও পড়ুন:
Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
Bari mu dauki dala a matsayin misali, tattalin arzikin Amurka na dogara ne kacokan da girman dalar Amurka. Yayin da kasafin kudinta ke gazawa wajen biyan bukatunta na cikin gida, kuma tana da al’adar dogaro da kasashen waje kan kudaden da take kashewa da ke da alaka da jingina gazawar mulkinta ga sauran kasashen duniya, kamar yadda ta yi a lokacin rikicin hada-hadar kudi na duniya a shekarar 2008, ta yaya masana’antunta za su farfado bisa wannan tsarin?
Hakazalika, babu yadda za a yi Amurka ta sake zama cibiyar masana’antun duniya bayan da ta yi watsi da matsalolin da ake fuskanta a zahiri kamar sauyin yanayi, wanda ayyukan masana’antu ne suka haifar da shi tun farko. Bari mu dauka cewa Trump zai iya cimma nasarar aiwatar da manyan gyare-gyare game da tsarin kasar lokaci guda, zuwa kyakkyawan tsarin siyasa da tattalin arzikin kasar duk da cewa akwai rashin jituwa tsakanin jam’iyyun kasar. Kana bari mu dauka cewa mutanen Amurka da ma duniya baki daya za su koma sayen yawancin kayayyakin da ake samarwa a Amurka. Har yanzu an bar mu da wata tambaya, shin za a samu isassun Amurkawa da za su yarda su yi aiki a masana’antunta, kuma za su yi hakan kan albashi mara tsoka idan aka kwatanta da sauran kasashen duniya, bayan da Trump ya kori kaso da dama na baki daga kasar ta Amurka? (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp