‘Yan Asalin Nijeriya Da Ke Buga Wa Kasashen Turai Wasa
Published: 9th, February 2025 GMT
Ga wasu manyan ‘yan kwallo da tauraronsu ke haskawa a duniya, wadanda asalin ‘yan Nijeriya ne, wato ko dai iyayensu baki daya ko wani daga cikin iyayen ‘yan Nijeriya ne.
Jamal Musiala (Jamus)
Matashin dan wasa Jamal Musiala, wanda aka haifa a ranar 26 ga Fabrairun shekarar 2003, fitaccen dan kwallon kasar Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich ta Jamus din kuma yana cikin matasan ‘yan kwallon da suke tashe a duniya a yanzu saboda ba za ka lissafa matasan ‘yan wasa guda biyar ba a duniya ba tare da ka saka sunansa ba.
Matashi Musiala ya wakilci kasar Ingila a kwallon matakin yara, kafin ya koma Jamus da buga wasa sannan kuma ya lashe kofuna da dama irin su gasar Bundesliga guda hudu da sauran kofuna, sannan ya samu kyaututtuka da dama tun daga lokacin da kungiyar Bayer Munchen ta fara saka shi a wasa tun yana dan shekara 17 a duniya.
Karim Adeyemi
Karim-Dabid Adeyemi wanda aka haifa a ranar 18 ga watan Janairun shekarar 2002, dan wasan Jamus ne da kungiyar kwallon kafa ta Borussia Dortmund. An haifi dan wasan a birnin Munich, wanda mahaifinsa asalin dan Nijeriya ne, amma mahaifiyarsa ‘yar Romaniya ne kuma a kwanakin baya danwasan da ke buga wasa a Dortmund da ke Jamus ya kusa komawa kungiyar kwallon kafa ta Napoli ta kasar Italiya kafin daga baya cinikin ya rushe bayan yaki amincewa da tafiya.
A baya-bayan nan Karim Adeyemi ya bude wata gidauniya a Nijeriya kuma ya bude gidauniyar ne a birnin Ibadan da ke Jiyar Oyo a kudu maso yammacin kasar nan, inda ya ce gidauniyar za ta mayar da hankali kan koyar da wasanni da ilimi, sannan a lokacin da ya ziyarci Nijeriya, Adeyemi ya shaida wa manema labarai cewa nan gaba yana tunanin komawa buga wasa a gasar Premier ta Ingila.
Michael Olise
Shima matashin dan wasan an haife shi ne a ranar 12 ga Disamban 2001, dan kwallo da a yanzu yake wakiltar Faransa kuma yake buga wasa a kungiyar Bayern Munich ta kasar Jamus. Olise wanda ya koma Jamus da buga wasa daga kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace asalin mahaifinsa dan Nijeriya ne, amma mahaifiyarsa ‘yar Aljeriya ce mazauniyar Faransa. Kuma yanzu haka yana daya daga cikin matasan ‘yan wasan da tauraruwarsu take haskawa a nahiyar Turai.
Noni Madueke
Shi dai asalin sunansa shi ne Chukwunonso Tristan “Noni” Madueke, kuma an haife shi ne a ranar 10 ga Maris a shekarar 2002 kuma yanzu yana wakiltar kasar Ingila ne, sannan yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta Ingila kuma shima asalin mahaifinsa dan Nijeriya, amma shi a Ingila aka haife shi, sannan itama mahaifiyarsa ‘yar asalin kasar Ingila ce.
Bukayo Saka
Bukayo Saka fitaccen dan kwallo ne da a yanzu yake jan zarensa a kungiyar kwallon kafa ta Arsenal da ke Ingila kuma danwasan wanda asalin sunansa Bukayo Ayoyinka Temidayo Saka, iyayensa Adenike da Yomi Saka duka ‘yan Nijeriya ne kuma a baya ya sha bayyana cewa yana alfahari da kasancewarsa dan Nijeriya, kuma ya kan ziyarci kasar nan a wasu lokutan.
Ethan Chidiebere Nwaneri
Ethan Chidiebere Nwaneri wanda aka haifa a ranar 21 ga watan Maris na 2007, matashin danwasa ne da a yanzu yake tashe a kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, kuma an haife shi ne a arewacin Landan, amma iyayensa ‘yan Nijeriya ne, sannan ya wakilci tawagar ‘yanwasan kasa da shekara 16 da 17 da 19 sai dai har yanzu ba wakilci babbar tawagar Ingila ba, wanda hakan ya sa za a iya gayyatarsa Nijeriya.
Joshua Orobosa Zirkzee
Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Bologna dake kasar Italiya, Joshua Orobosa Zirkzee wanda aka haifa a ranar 22 ga Mayun 2001, dan kwallo ne da yake wakiltar kasar Netherlands, kuma yake buga wasa a yanzu a kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta Ingila sanann an haife shi ne a birnin Schiedam, sai dai shi mahaifiyarsa ce ‘yar Nijeriya, amma mahaifinsa dan Netherland ne.
কীওয়ার্ড: a kungiyar kwallon kafa ta wanda aka haifa a ranar yan Nijeriya ne dan Nijeriya buga wasa a
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce matakin da gwamnatin Isra’ila ta dauka a kan kasar tamkar shelanta yaki ne.
Araghchi ya bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ya aikewa babban sakatare na MDD da kuma shugaban kwamitin sulhu bayan da Isra’ila ta kai munanan hare-hare kan wuraren soji da cibiyoyin nukiliya da kuma wuraren zama wanda ya yi sanadiyar mutuwar wasu manyan kwamandojin dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), masana kimiyyar nukiliya da fararen hula na iran.
“Wadannan ayyuka na zalunci ba wai kawai sun zama babban cin zarafi ne ga ‘yancin kan kasar Iran a matsayinta na mamba mai cin gashin kanta a Majalisar Dinkin Duniya ba, amma kamar yadda dokokin kasa da kasa da dokokin jin kai na duniya, ciki har da yarjejeniyar Geneva, suka tanada wannan na daga cikin ayyukan wuce gona da iri da laifukan yaki.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya sauke nauyin da ke wuyansa, ya yi kakkausar suka ga wannan ta’addanci tare da daukar matakin gaggawa kan Isra’ila.
Ya kara da cewa “Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki da cikakkiyar azama wajen kare ‘yancinta, al’ummarta da kuma tsaron kasarta. Wannan wani hakki ne da ba za a iya tattaunawa da shi ba.”
Daga cikin hare-haren da ta kai, Isra’ila ta kai hari kan Cibiyar Nukiliya ta Natanz da ke tsakiyar kasar Iran, wadda ke aiki karkashin cikakken kulawar Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA), in ji shi.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi gargadin cewa hare-haren ta’addanci na gwamnatin Tel Aviv na jefa rayuwar fararen hular Iran cikin hadari tare da haifar da barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.