HausaTv:
2025-05-01@04:43:43 GMT

Kissoshin Rayuwa Imam Hassan (s) 12

Published: 9th, February 2025 GMT

12-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa Shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na shahid Aya. Murtadha muttahhari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen ,Rumi, ko kuma cikin wasu littafan.

Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan (s) limami na 2 daga cikin limamai masu tsare daga iyalan gidan manzon All..(s) kuma dan Fitima(s) diyar manzon All..(s) na farko.

Kuma a cikin shirimmu da ya gabata mun yi maganar yadda manzon All..(s) bayan kwanaki kadan da komawa Madina sai All..ya umurceshi da ya ji makabartan Bakiyya, ya nema masu gafara, don haka a cikin dare ya kira daya daga cikin yentattun bayinsa wanda ake kira Abu Maubihah inda ya fada masa cewa an umurce ni in nemawwa mutanen makabartan bakiyya gafara daga wajen All ..T kuma ina son ka rakani.

A lokacinda suka isar makabartan sai ya fadawa Abu Maubihah kan cewa an bani zami na mubudan taskokin duniya har abada, sannan aljanna, ko kuma haduwa da All..,amma na zami haduwa da All..,

Daga karshe ya zami haduwa da All..T. Sannan bayan kwanaki kadan, sai fara rashin lafiyarsa ta karshe, a nane sai yayi tunanin yadda iko zai koma ga Aliyu dan Abitalib (a) bayansa da sauki. Sai ya tada rundunar Usama dan Zaidu, ta tara dukkan manya-manyan sahabbansa daga cikin muhajirun da ansar, ya dora Usama dan shekara 17 a kansu.

A ciki ya umurci shi da yaje kasar Ruma ta gabas inda aka kashe babansa, ya yi kafirai.

Ya nuna masa dukkan dabarbarun yaki. Sannan ya bashi tutar, sai Usama yake wani wuri a bayan madina wanda ake kira Jurf. Sai yace masa. Amma suka ki fitowa su same shi, wasu ma suka fara sukan shugabancin Usama dan Zaidu, a lokacinda labari ya zo masa wasu sunki fita, sannan suna sukan shugabancin Usama a nan ma sai ya sake fita ya kuma yi masu Magana ya sake jaddada cewa, usman a ya canacanci shugabanci, haka ma babansa kafin shi. Duk da cewa a lokacin ma sun ki amincewa da jagorancin bababansa.

Mun kawo fara kawo maku abinda zamu iya dauka a cikin wannan hadisin, na cewa dabarar da manzon All..(s) yayi na nisantar da masu kodayin Mulki a bayansa ba zai kai ga nasarab, sannan su ma sun fahinci haka, shi ya sa suka sabawa manzon All..(s). Bayan haka.

Mun ji cewa a cikin manya-manyan sahabban da ya Sanya a cikin rundunar Usama akwai, Abubakar, da Umar da Abu ubaida dan jarrah da Usman da sauransu.

Sanna yaki sanya su kan rundunar ne don kada, wani daga cikinsu ya yi amfani da wannan damar don biyar bukatuna sa na kaiwa da shugabanci a bayansa.

Don haka ya tushe masu hanya, sannan ya la’ani duk wanda ya ki tafiya da rundunar Usama.

Banda haka wata dubarar da manzon All..(s) ya yi na shugabantar da Usama dan Zaidu  kan wadannan manya-manyan sahabban, shi ne ya nuna masu cewa, shugabanci cancanta ne ba yawan shekaru ba. Kuma All..ya na bawa shugabanci ga wanda ya ga dama, kuma zai bashi ilmi da kuma karfin da yake bukata don cancantar shugabancin.

Don haka manzon All..(s) ya bar wannan duniyar, manya-manyan sahabban manzon All..(s) su na karkashin shugabancin Usama dan Zaidu wanda bai fi shekaru 17 a diniya ba.

Don haka me zai hana Aliyu dan Abitalib wanda ya Usama shekaru, wato dan shekara 30 a duniya a lokacin, zama khalifan manzon All..(s) a bayansa(s)?.

A wani hadisi manzon All..(s) ya na cewa: wanda ya gabatar da kansa a cikin musulmi al-hali ya san da cewa akwai wanda ya fi cancanta da aikin to hakika ya kha’inci All..da manzonsa dakuma muminai (s).

A wani hadisin, yana cewa: All..yana kudaitarwa, sosai kan, wajen zaben mafi korewar mutane,  wanda ya kasance mafi cancanta ga wani matsayi. Lalle su sanya maslahar al-umma ne abin lura wajen zaben wanda ya cancanta. Su kasance amintattu a cikin abinda suke karba daga hannun mutane. A cikin cikin kuma kudaden da suke kasewa don abubuwan ji dadin rayuwar mutane. Sannan su tafiyar da al-amuran mutanen a cikin adalci kadai.  

Wannan kada ya kasance da yawan shekaru, sai dai ya kasance tare da kwarewa da kuma sanin makamar aiki, da sanin abubuwan da mutane suke bukata.

Don haka manzon All..(s) a cikin shugabantar da Usama Dan Zaidu ya kakkabo wasu daga cikin wadanda suke takara da Amirulmuminina (a) kan shugabancin al-ummar musulmi.

Ya karya zukatansu, daga neman wannan mukamin, ya kuma kashe guiwarsu daga ynkuri don neman wannan matsayin. Ya nisantar da su nesa ba kusa ba daga wannan burin nasu. Sannan suma sun fahinci haka a wajen manzon All…(s) kan hakan.

Baku ga cewa, Umar yana cewa Usama! Manzon All.. zai yi wafati kana shugabana?  Basu gushe ba suna suna jan kafa, sun ci gaba da sabawa manzon All..(s) har sai da ya yi wafata. (s).

Wannan kadan Kenan na abinda za’a iya fahinta na shugabatar da Usama dan shekara kimani 17 kan shaihunan kurasihawa da kuma wasu shuwagabannin ansar wadanda suka kodayin shugabancin al-ummar musulmi bayan wafatin sa (s).

Har’ila yau wannan ya tabbatar mana akwai makirci babban da aka kulla don hana Imam Ali (s) zama a kan kujerar da shi kadai ya dace da ita bayan manzon All..(s).

Zazzabi ta yi tsanani ga manzon All..(s), a lokacin matansa suka kusa da shi, a duk sanda suka sa hannunsu a kansa suna jin zafin jikinsa.

Sun sanya ruwan sanyi kusa da shi, a duk sanna ya sa hannunsa cikinsa sai ya taba ruwan ya shafi kansa da hannunsa.

Sai mutane suna ta kai kawo suna bankwana da shi, sai da suka taru a gidan sai yana fada masu: Ya ku mutane, an kusa a dauki raina, daukewa mai sauki, a tafi da ni. Hakikin na gabatar da maganganu, don sauke uzuri da ke kaina a kanku. Sai dai lalle ni ina barin Littafin All..mai girma da daukaka da kuma zurriyata Ahlubaiti na.  Sai ya kana hannun Aliyu(a) ya daga ta. : Sai yace: Ga Aliyu nan tare da Alkur’ani , kuma kur’ani yana tare da Ali ba zasu rabu ba, har sai sun riskeni a tabki.

Abinda yakamata al-umma ta yi shi ne ta bi umurnin manzon All..ta bi abinda ya fada mata ta bi Amirulmuminina (s), ta mika mata shugabanci, don shi ne kawai zai tafiyar da al-amarinsu kan koyarwar Alkur’ani mai girma. Ya kuma yi hukunci da hukuncin All..

Ta ta yi haka kuwa da ta tsira daga dukkan tawaya, kuma fitinu ba zasu same ta ba haka ma dukkan hatsurra ba zasu sameta ba. Da kuwa musulunci zai taka matakansa kai tsaye tare da daukaka ya kuma sami iko da duniya gaba daya. Ya cika shi da adalci.

Har’ila yau kafin rasuwarsa manzon All..(s) ya daura rawaninsa, sai ya je masallaci ya hau mimbarinsa, sai yace masu, Lalle Ubangijina ya hukunta ya kuma rantse kan cewa ba zai yafe zulunci azzalumi ba, don haka ina hadaku da All…duk wani mutum wanda yake da wani abu da na yi masa sai ya tashi ya fada don yayi kisasi, a yi kisasa a gidan duniya yafi mani da kisasa a Lahira. A gaban mala’iku da annabawa…}.

Sai kowa ya kasa Magana, manzon All..(s) yana nuna masu kan cewa zalunci ko wace irice mutum ya warware shi a lduniya ya fi masa a yi masa adalci a lahira.

An dade ba wanda yayi Magana sai wani mutum daga karshen masallacin mai suna Sawadat dan Qais, sai yace ai manzon All..(s) ya taba dokansa cikinsa wani lokaci don haka yana son kisasi.

Sai manzon All..(s) yace masa ya zo . sannan ya aiki Bilala ya kawo bulala a gida, da ya kawo sai mutana suna gani me mutumin nan za iyi da manzon All..(s) a cikin wannan halin da yake na rashin rafiya.

Sai Sawada ya zo kusa yana karkarwa., saboda haibar manzon All.. sai y ace: Ya manzon All..ka kyaye mani cikink, sai ya ce ya manzon All..(s) kayi mani izini in Sanya bakina a kan cikinka, sai yace masa ee. Sai ya Sanya bakinsa a kan cikin manzon  All… idanunsa yana zubar da hawaye. Sai yana cewa  ina neman tsari daga wuta albarkan wurin kisashi daga manzon All..(s), a ranar lahira.

Sai manzon All..(s) ya ce masa, zaka yi kissasi ne ko kai yi afwa, ya swadatah sai y ace Afwa ya manzon All..(s). 

Sai manzon All..(s) yad aga hannayensa masu albarka yana uddu’a yana cewa: Ya Ubangiji ! ka gafartawa Sawadatah saboda afwan da yayi wa annabinka Muhammadu.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu . wassalamu Alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: manya manyan masu sauraro

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja

Rayukan al’umma gami da dukiya musamman na ababen hawa na ci gaba da salwanta a Mahadar hanya ta yankin Tipper-garage da ke Dutse-Baupma, da ke kan titin da ya tashi daga garin Dutsen-Alhaji ya nufi garin Bwari, a yankin Birnin Tarayya Abuja.

Titin da ke mastayin tagwaye ya haɗa yankin da garin Jere da ke Jihar Kaduna.

Hanyar na ci gaba da ganin ƙaruwar kwararan motoci a sakamakon ingancinta da kuma karancin matsalar tsaro, idan a ka kamanta ta da babban titi Abuja zuwa Kaduna.

Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027 An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas

Adadin motoci da ke bin titin ya kara dagawa a bayabayan nan a dalilin mummunan cunkushewar hanya da ake fuskanta a garin Zuba Abuja da kuma Madalla da ke Jihar Neja, a sakamakon rufe hannu guda na hanyar biyo bayan fara aikinsa da wani sabon kamfani ke yi, bayan karbe aikin daga kamfanin Bega.

Baya ga motoci na matafiya da ke yawan ratsawa ta hanyar, akwai kuma motocin tifa da ke daukar duwatsu daga kamafanonin fasa duwatsu biyu da ke kusa da mahadar hanyan suna kai wa yankuna daban-daban na Abuja dama kewaye.

Aminiya ta ba da labarin cewa hatsarin mota na baya bayan nan da a ka fuskanta a hanyar su ne wanda ya auku a ranar Asabar 5 ga wannan watan na Afrilu, 2025, inda a ka rasa rayukan mutum biyar, bayan wata babbar mota tirela da ta fito ta kusurwan Bwari ta fuskanci matsalar tsinkewar birki a yayin da ta ke gangarowa daga hayin madatsar ruwa na Usuma dam da ke kan titin.

Tirelar ta taka kekunan adaidaita sahu guda biyar da ke daukar fasija a gefen hanayar, baya ga wani adadi na baburan acaba.

Kwana biyu bayan aukuwar hatsarin, an sake fuskantan wani a ranar Litinin da ta biyo baya inda wata babbar mota irin ta daukar bulo da ke dauke da albasa daga wata jiha ta Arewa ta rasa birki a yayin saukowa daga gangarar hanyar.

Ta buge kekunan kafin ta kife a kusa da wani magudanan ruwa da ke jikin hanyar.

An bada labarin rasa mutum biyu a yayin hatsarin, baya ga wasu da su ka tsira da raunuka.

Asarar rayuka da ta dukiya da muka yi — Masu tukin adaidaita sahu

Malam Fahad Musa na cikin shugabannin kungiyar ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin Keken Adaidaita sahu da ke aiki a wurin.

Ya ce hatsarin farko ya faru ne da misalign karfe 7 na dare inda ya ce sun rasa mambobinsu uku, sai kuma dan acaba guda, a yayin da mutum na biyar din kuwa ya rasa ransa ne a dalilin harbinsa da bindiga da ake zargin wasu da suka taho cikin ayarin motoci suka yi, kamar yadda majiyoyi daban-daban suka shaidawa Aminiya.

Shugaban na ’yan yuniyon ya shaida wa wakilinmu a yayin ziyara a wajen cewa an kuma rasa kekune biyar a yayin hatsarin bayan motar ta bi ta kansu.

Ya ce faduwar motar ta farko ta yi sanadiyyar rufe hannu guda sannan ba a kai ga cire ta ba sai bayan hatsari na biyu a ranar Litinin.

Ya ce, a lokacin da ake kokarin zakulu mutane da suka mutu da kuma wadanda suka yi raunukan daga karkashin ababan hawan a ranar Asabar, an rufe daukacin tagwayen titin biyu da lamarin ya kai ga jawo takaddama bayan ayarin jami’an tsaro sun bulla ta wajen.

Wani da ya shaidi lamarin, ya shaida wa Aminiya cewa, a lokacin da ayarin motocin suka bullo, wani babba a cikin tawagar ya fito daga cikin mota tare da neman da a bude masu daya hanyar, amma sai ’yan asalin al’ummar yankin suka ki amincewa da bukatar hakan.

Ya kara da cewa, matasan sun bi motocin ayarin da jifa bayan sun kutsa ta daya hanyar da nufin wucewa, kuma a nan ne sai wasu daga cikin jami’an tsaron suka yi harbi cikin iska, a yayin da wani kuma ya harbi daya daga cikin matasa ’yan asalin yankin mai suna Timothy John, da ya mutu nan take.

Bayan nan, ayarin sun wuce da motocinsu cikin hanzari, kamar yadda aka bayyana wa Aminiya.

A yayin zantawarsa da Aminiya shugaban n ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin adaidaita sahu ya ce, daya daga cikin direbobinsu mai suna Yusuf Auwal na cikin wadanda harsashin bindiga ya bi ta jikinsa.

Ya ce, bayan nan an garzaya da shi zuwa garinsu inda yake cigaba da jinya a yanzu.

Babban Kwamandan Hukumar Kare Hadurra na FRSC mai kula da yankin Dutsen-Alhaji, Mista Luka Wuna, ya tabbatar da faruwan haduran biyun, da kuma rasa rayukan, a yayin zantawarsa da wakilinmu a kan lamari.

Akwai bukatar ilimantar da direbobin Tifa

Binciken Aminiya ya bayyanan cewa, matsalar da tifofi ke samu ta shanyewar burki a yayin da suka ɗauko kaya kuma suka sukwano gangarar da daga ita sai marabar titin ita ce a mafi yawan lokaci ke haddasa munanan hadurra a wannan mahada.

Da yawan direbobin tifa matasa ne da basu san dokokin tuki ba sannan kuma suna tukin da ganganci tamkar suna tuka kananan motoci.

Don haka mafi yawa ba sa kula da yadda suke shawo wannan gangara ta la’akari da cewa, burkin tifa iska ce.

Wani masanin harkokin sufuri da ba ya son a ambaci sunansa ya ba da shaara cewa, ya kamata hukumomin da abin ya shafa su rinka shirya wa direbobin musamman na Tifa bita kan ka’idojin tuki da alamomin hanaya da kuma hatsarin da ke tattare da burkin mota mai dauke da iska.

Abinda ke jawo hatsari a wajen

Malam Anas Mu’azu na cikin ma’aikatan tattara haraji na Karamar Hukumar Bwari da ke ba da tikiti a wajen.

Ya ce, yawancin direbobi da ke fuskantar hatsarin baki ne da ke bi ta gangaren hanyar ba tare da cikakken masaniya a kan yadda wajen yake ba.

Ya ce, ”wutar ba da umarnin wucewa a wajen da ke da kusurwa 4 na bukatar tsayawar mota na wani lokaci a duk ta inda ta fito saboda dogon layi da motoci ke yi, sannan indan wutar ta haska don wucewa, adadi kadan ne na motoci ke iya wucewa kafin ta sake bukatar tsayar da mota,” in ji shi.

Malam Anas ya kara da cewa yawancin bakin direbobi da ke bin hanyar ba su da masaniya a kan tsarin wutar da kuma yanayin hanyar kasancewar babu allunan alamomi na hanya da ke fadakarwa a kan titin.

Ya ce, haka kuma a baya an cire kunyar kan titi da ke sa motoci rage gudun mota. ”A baya akwai kunyar titi na rage gudun da adadinsu ya kai kamar guda biyar, amma sai a ka cire su a lokaci guda ta hanyan kankare su daga kan hanyar,” in ji shi.

Ya ce, ko da Ministan Birnin Abuja Mista Nyesom Wike ya ba da aikin sake gina hanyar a bayabayan nan, ba a maida kunyar titin ba, har zuwa lokacin da haduran baya-bayan nan su ka auku..

Yadda za a magance matsala —Masu Tifa

Haka kuma Aminiya ta zanta da daya daga shugabannin masu motocin tifa da kuma harkar sayar da duwatsu daga kamfanoni biyu na fasa dutsi da ke yankin mai suna Kwamred Ose Idasho inda ya ba da shawarwaari kan yadda ya ke ganin za a magance yawaitar haduran, da ya ce sun bayar a yayin wani zama na musamman da Jami’an Hukumar Magance Hadurra ta FRSC a yankin.

Ya ce, “abu na farko shi ne bukatar a sa alamomin hanya tun daga kamar kilo mita uku kafin mahadar hanyar da zai rika sanar da direba hatsarin wajen tare da bukatar da ya yi takatsantsan.

“Sai kuma a sa abubuwa da ke sa rage gudun mota na kunyar hanya samfurin roba ba na siminta ba, da zai rika yin kara idan direba ya yi yunkurin yin gudu sosai. Hakan zai kara wa direba karsashi ko da ya fara yin gyangyadi.

“Mun kuma bukaci jami’an na FRSC da nemi dauki daga Hukumar Kula da Gine-gine ta Abuja kan su kawar da wuraren da ke sa mutane na tsayawa ta wurin, tare da mayar da shi sarari, sai kuma samar da wurearen yin lodi da kuma hana yin lodi a gefen titin.

“Haka kuma akwai bukatar a gyara wasu daga cikin fitilun ba da hannu da suka daina yin aiki, kamar wanda ya shiga ta bangaren Bamuko ta inda motocin tifa ke shiga da kuma yawan fita.

Sai kuma uwa-uba a gina gadar sama a wajen da zai rage girman gangarowar motoci da ke fitowa ta kusurwar Bwari ko DutsenAlhaji inda motocin za su bi ta saman gada,” in ji jagoran masu motocin tifa.

Ya kamata a gina gadar sama

Shi ma a zantawarsa da Aminiya, Sakataren Hakimin yankin na Dutse-Baupma mai suna Simon Luka da ya yi bayani a madadin hakiminsu, ya ce, hatsarin motoci a wajen ya jima yana jawo masu fargaba da kuma asarar rayuka da dukiya.

Ya buƙaci Ministan Birnin Tarayya Mista Nyesom Wike da ya taimaka wajen yin aikin gadar sama a wajen don magance matsalar.

Ya ce, tarihin farawar matsalar ba za ta gaza shekara 20 bayan an yi aikin hanyar.

Ya ce, matashin da aka kashe bayan jami’an tsaro sun buɗe wuta a wajen mai suna Timothy John, bai wuce shekara 20 ba kuma lamarin ya faru ne kasa da mako guda bayan mai gidansa ya yaye shi daga aikin walda da ya ke yi, inda yake shirin buɗe na kansa.

Ya kara da cewa, “sai dai har zuwa lokacin ziyarar nan babu wata ta’aziyya ko ta jaje da muka samu daga jamiu’an tsaro ko kuma hukuma, kan mutuwar matashin.”

Aminiya ta tuntubi Babbar Jami’ar Hulda da Jama’a a Sakatariyar da ke Kula da Sufuri a yankin Birnin Tarayya Abuja mai suna Misis Lecita Wogu, inda ta buƙaci lokaci don yin tsokaci a kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115