Shugabannin Kudanci Da Gabashin Afrika Sun Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Wuta A gabashin DRC
Published: 9th, February 2025 GMT
Shugabannin kungiyoyin raya kasashen gabashi da kuma kusanci na Afrika (EAC da SADC), sun yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a gabashin Jamhuriyar DR Congo.
Bangarorin sun bayyana hakan a wani taron hadin guiwa da suka gudanar a birnin Dar es Salaam, na kasar Tanzania a jiya Asabar.
A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar, sun kuma bukaci da bude manyan tituna da filin jirgin saman Goma, da kuma tattaunawa kai tsaye tsakanin Kinshasa da kungiyar M23.
Saidai taron, bai yi Allah wadai da Rwanda ba kan shigar ta cikin rikicin ba.
Taron na hadin gwiwa ya tabbatar da hadin kai da jajircewa wajen ci gaba da marawa DRC baya a kokarin da take yi na kare ‘yancin kanta, da ikonta da kuma yankunanta,” a cewar sanarwar karshen taron.
A nata bangaren, tawagar ta Rwanda ta yi imanin cewa, wannan taro ya cika burin Kigali.
Wanda ya bada dama don dawo da zaman lafiya a gabashin DRC”, a cewar ministan harkokin wajen kasar a shafinsa na X.
“Taron na hadin gwiwa ya bukaci shugabannin rundunar tsaro ta AEC (Al’ummar Gabashin Afirka) da SADC (Al’ummar Gabashin Afirka ta Kudu) da su gana cikin kwanaki biyar don fidda hanyoyin tsagaita wuta ba tare da wani sharadi ba da kuma dakatar da fada.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
An fara kasuwar baje koli na kayakin kasuwancin da ake samarwa a cikin Iran ko IRAN EXPO 2025, karo na 3 a nan Tehran.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kasuwar baje koli na Iran EXPO 2025 zai jawa masu zuna jari daga kasashen Afirka.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya fadawa kamfanin dillancin labaran IP kan cewa Kasuwar ta bana dai, za ta tara kamfanonin masu samar da kayaki daga yankuna daban daban na kasar Iran da dama, kuma akwai fatan cewa wannan kasuwar ta zama mabudi ga kyautatuwan tattalin arzikin kasar.
EXPO dai ita ce kasuwar baje koli na kayakin kasar Iran mafi girma wanda ake gudanarwa a ko wace shekara, sannan daga nan take samun kasuwa a kasashen duniya. Kuma yan kasuwa daga kasahe fiya da 100 ne suka shigo kasar don halattan kasuwar.
Esma’il Bakaee, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya ce ya na fatan a wannan kasuwar, kasashen Afirka da Iran za su amfani juna a harkokin kasuwancin da ake bunkasa a tsakaninsu.