Leadership News Hausa:
2025-09-17@23:17:32 GMT

Yadda Za Ku Magance Kaikayin Gaba

Published: 8th, February 2025 GMT

Yadda Za Ku Magance Kaikayin Gaba

 

Yadda ake amfani da shi:

Za ku dinga shafa zumar a gabanku, ku barta na tsawon mintuna 30, sai ku wanke da ruwan dumi, sannan ku shafa Man Zaitun. Za ku dinga yin haka safe da  yamma kafin kwanciya.

Sannan ku dinga dafa ‘ya’yan hulba na tsawon mintuna 10 da ruwan da bai wuce kofi daya ba, sai ku dora shi a wuta ya dan tafasa bayan kun sauke shi sai ku tsiyaye shi sai ku sa masa zuma cokali uku, za ki yi wannan hadin shima safe da yamma.

 

Sai kuma maganin kurajen da kaikayin gaba:

Kai tsaye ana cewa sanyin mara shi ne yake jawo wannan matsala, amma abin da ya kamata mu sani shi ne ba iya shi kadai yake jawowa ba akwai abubuwa da dama.

Akwai abubuwa da yawa da ke haifar da wannan matsala, bayan kamuwa da cuta da akan ce yana haifar da wannan matsalar, akwai wasu abubuwa a bayansa.

Wani lokacin sanya kaya ko ‘Underwear’ wanda ya matse ka yana jawo kaikai wani kuma motsa jiki ko tafiya mai nisa a kafa ko gudu suna jawo masa wannan.

Akwai karancin tsafta, mutum ya rika sanya ‘Underwear’ kusan mako guda ba tare da an canza shi ba, wasu kuma ba sa barinsu su bushe bayan sun yi wanka sannan su sanya tufafi, duk suna haifar da wannan matsala.

Koda gaban dadewa yake yana saba yana wari in sha Allah idan akai wannan za’a samu waraka

 

Abubuwan da ake bukata:

Man Darbejiya, Man tafarnuwa, Man zogale, Man kwakwa:

 

Yadda ake hadawa:

Da farko za ku samu kowanne daga cikinsu, amma ku tabbata kun samu na asali masu kyau saboda biyan bukata, kuma kowanne yana samuwa a Islamic chemist.

Idan kuka saya kowanne, ku auna shi da murfin kwalbar.

Sai a hada su waje daya a shafa a wurin da kurajen ya bayyana ga namiji, idan ya takura sai a bar shi, sai a yi wanka a bar shi ya bushe, sai a shafa wannan maganin a wurin sannan a sa tufafi, sai a yi kokarin canza rigar a kowane kwana 2.

Idan mace tana da kuraje ko kamuwa da cuta na dogon lokaci ko kamuwa da cuta, sai ta samu auduga ta shafa mai a jikinta idan ta kwanta ta danna gabanta kuma a sha ruwan dumi, a guji shan ruwan sanyi. Allah ya sa mu dace.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025

Gwamnatin Jihar Jigawa  ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na Naira Biliyan 75 na shekarar 2025, ga gwamnatin jiha da kuma ƙananan hukumomi 27.

Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan zaman majalisar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa, wannan ƙarin kasafin kuɗi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga domin biyan buƙatun kuɗaɗen da suka taso, da kuma ƙarfafa manyan fannoni da za su kawo ci gaba mai ɗorewa a faɗin jihar.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, majalisar ta amince da Naira Biliyan 58 ga gwamnatin jiha da kuma Naira Biliyan 17 ga Kananan Hukumomi 27, wanda ya shafi kashe-kashen kudade na yau da kullum da kuma manyan ayyuka.

Ya ce, wannan ƙarin kasafin kuɗin zai inganta ayyuka da tsare-tsare da ake gudanarwa a muhimman fannoni irin su ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, noma da sauran muhimman ayyukan ci gaba.

Sagir ya ƙara da cewa, za a mika ƙarin kasafin kuɗin ga Majalisar Dokokin Jihar domin tattaunawa da amincewa da shi, kamar yadda kundin tsarin mulki da ka’idojin kasafi suka tanada.

Kwamishinan ya ƙara jaddada cewa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen gudanar da mulki bisa gaskiya da adalci, da kula da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace, da kuma tabbatar da samar da ingantattun ayyuka ga al’ummar jihar baki ɗaya.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta