Kudin Ajiyar Najeriya Na Kasashen Waje Sun Ragu Da Dalar Amurka Biliya 1.79
Published: 7th, February 2025 GMT
Bayanin da babban bankin kasar ta Najeriya ya fitar, ya bayyana cewa an sami wannan koma bayan ne a cikin makwanni uku da su ka gabata.
Bayanin na babban bankin na Najeriya ya ci gaba da cewa, kudaden ajiyar Najeriya na waje da a cikin watan Disamba sun kai dala biliya 40,887, sun ragu, sun zama dala biliyan $39.
An bayyana koma bayan ne a kudaden waje na ajiya da babban bankin kasar yake da su, da ya kamata ace a ranar 4 ga watan Febrairu ne za a fitar da kididdiga akan halin da kudaden wajen suke ciki,amma ba a yi ba.
Bugu da kari wannanbayanin ya fito ne daga kamfanin dake kula da kai da komawar kudaden Waje Bismack Rewane da yake hasashen samun raguwar kudaden ajiyar na Najeriya a tsakanin shekarar 2025-2026 sai sami koma baya da kaso 11.47,wato zuwa dala biliyan 36.21, yayin a a cikin shekarar 2026 zai zama dala biliyan 37.65,alhali a 2024 ya kasance dala biliyan 40.9.
Farashin Naira idan aka kwatanta ta da Dala, a 3 ga watan nan na Febrairu shi ne ; Naira 1,500.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dala biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Bakai’i: Iran Tana Son Ganin An Yi Taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa;Yunwar da mutanen Gaza suke fama da ita na tsawon watanni biyar, laifi ne maras tamka da HKI take tafkawa, da ya zama wajibi kungiyar kasashen musulmi ta yi taron gaggawa akansa.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran Dr. Isma’ila Baka’i wanda ya gabatar da taron manema labaru a yau Litinin ya kuma yi Magana akan tattaunawar da Iran ta yi da kasashen turai akan shirinta na makamin Nukiliya, ya ce: Tattaunawar da aka yi ta da kasashen turai manufarta ita ce dauke wa Iran takunkuman da aka kakaba mata akan shirinta na Nukiliya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya kuma ce; Kasashen na turai ba su da hakkin su kakabawa Iran takunkumi, idan kuwa har su ka ci gaba to za su fuskanci mayar da martanin Iran.