Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sauye-sauyen shugabanci a jami’o’in gwamnatin tarayya da dama da suka hada da Jami’ar Abuja wadda a yanzu ake kira da Jami’ar Yakubu Gowon.

 

A wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai Bayo Onanuga ya ce a jami’ar Yakubu Gowon, shugaba Tinubu ya rusa majalisar zartarwa gaba daya tare da sauke Farfesa Aisha Sani Maikudi daga mukaminta na shugabar Jami’ar.

 

Sanata Lanre Tejuoso, wanda a halin yanzu shi ne uban Jami’ar Aikin Gona ta Makurdi ne aka nada shi a matsayin Uban Jami’ar Yakubu Gowon. Sanata Joy Emordi, wacce a yanzu ita ce shugabar jami’ar ilimi ta Alvan Ikoku za ta gaje shi a Makurdi.

 

Shugaba Tinubu ya nada Farfesa Lar Patricia Manko a matsayin mukaddashiyar shugaban jami’ar Yakubu Gowon na tsawon watanni shida. Ba za ta cancanci neman matsayin Shugabancin Jami’ar ba idan aka tashi neman shugaba.

 

Bugu da kari, shugaba Tinubu ya cire Farfesa Polycarp Emeka Chigbu daga mukaminsa na Shugaban jami’ar Nsukka (UNN), kafin wa’adinsa ya kare a ranar 14 ga watan Fabrairu.

 

An nada Farfesa Oguejiofu T. Ujam a matsayin magajinsa na tsawon watanni shida kuma ba zai cancanci neman mukamin na dindindin ba.

 

Gen. Ike Nwachukwu ya koma Uban Jami’ar Uyo. Shugaba Tinubu ya nada Injiniya Olubunmi Kayode Ojo a matsayin sabon shugabar UNN. A baya, Ojo ya rike wannan matsayi a Jami’ar Tarayya ta Lokoja da Jami’ar Tarayya ta Oye-Ekiti.

 

Farfesa Zubairu Tajo Abdullahi, wanda a halin yanzu shi ne Uban Jami’ar Uyo, an nada shi ya gaji Ojo a Jami’ar Tarayya ta Lokoja.

 

Sanata Sani Stores shi ne sabon Shugaban Jami’ar Ilimi ta Alvan Ikoku, wanda ya gaji Sanata Joy Emordi. Sanata Stores dan majalisa ne a Jami’ar Najeriya, Nsukka.

 

Bugu da kari kuma, Barista Olugbenga Kukoyi, wanda dan majalisa ne a jami’ar Najeriya, Nsukka, an nada shi a matsayin sabon shugaban jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke Awka a jihar Anambra.

 

Sanarwar ta bayyana cewa duk nade-naden mukamai sun fara aiki ne nan take.

 

Shugaba Tinubu ya jaddada cewa, wadannan sauye-sauyen na nuni da kudirin gwamnatinsa na farfado da harkar ilimi mai zurfi a Najeriya ta hanyar jagoranci da rikon amana.

 

Sanarwar ta kara da cewa sake fasalin na da nufin karfafa harkokin mulki da nagartar ilimi a bangaren ilimin manyan makarantun Najeriya.

 

 

Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jami ar Yakubu Gowon jami ar Yakubu Gowon Shugaba Tinubu ya

এছাড়াও পড়ুন:

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

An garzaya da shi zuwa babban Asibitin Gwamnatin Tarayya da ke Birnin Kebbi, inda daga bisani likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.

An yi jana’izarsa a babban masallacin Sarkin Gwandu, sannan aka binne shi a makabartar Dukku da ke kan hanyar Makera zuwa Kangiwa.

Jana’izar ta samu halartar jami’an kwas5tan, ‘yan uwa, abokai da sauran mu5sulmi daga sassa daban-daban na jihar.

Har yanzu al’ummar garin Filgila da kewaye na cikin tashin hankali da fargaba, kasancewar hare-haren Lakurawa na jefa su cikin zulumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin