Afirka Ta Kudu Ta Dage A Kan Matsayinta Duk Tare Da Barazabar Amurka Na Kin Halattan Taron G20
Published: 7th, February 2025 GMT
Gwamnatin kasar Afirka ta kudu ta ki bada kai ga bukatun Amurka duk tare da barazanar sakataren harkokin wajen kasar Marco Rubio na fasa zuwa taron G20 a kasar
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ronald Lamola ministan harkokin wajen kasar Afirka ta kudu na cewa
“kasarmu yentacciyar kasa ce, kan tsarin democradiya, sannan tana mutunta bil’adama, tana daidaito tsakanin kasa, babu bambamcin launin fata”
Lamola ya kara da cewa kasarsa na da tsarin zamanta kewa mai cikekken yanci daga duk wata kasa a duniya.
Ministan ya kara da cewa, ba sauyin yanayi ne kawai muke tattaunawa a taron G20 ba,
Kafin haka sakataren harkokin wajen Amurka yace, shi ba zai halacci taro inda babu ambaton bukatun Amurka ba.
A ranakun 20-21 na watan Fabrayrun da muke ciki ne za’a gudanar da taron G20 a birnin Jorhamsboug na kasar Afirka ta kudu.
Amma Amurka tana korafin yadda Afrika ta kudu tasa HKI a gaba, kan kisan kiyashin Gaza da kuma wata dakar wacce shugaban kasar Cyril Ramaposa ya sanyawa hannu dangane da rabon filaye cikin adalci a kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta ce mayar da martani ga gwamnatin Isra’ila hakki ne na shari’a ga Iran kamar yadda doka ta 51 ta kundin tsarin mulkin MDD ta tanada.
Da farko dai ma’aikatar ta mika ta’aziyyar shahadar wasu kwamandoji da jami’an kasar Iran a harin da Isra’ila ta kai wa kasar.
“Hare-haren da gwamnatin sahyoniyawan ta kai wa Iran sun sabawa doka ta 4 sakin layi na 2 na kundin tsarin mulkin majalisar dinkin duniya a matsayin wani mataki na wuce gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma Iran tana da hakki na shari’a na halal ta mayar da martani kan wannan zalunci kamar yadda yake a cikin sashe na 51 na kundin tsarin mulkin majalisar dinkin duniya.
Sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kare al’ummar Iran da dukkan karfinsu.”
“Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na mamba a Majalisar Dinkin Duniya, tana mai jaddada wajibcin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya na daukar matakin da ya dace wajen tunkarar matsalar zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa, sakamakon wuce gona da iri da gwamnatin sahyoniyawan take yi wa Iran.
“Dukkan kasashe mambobin Majalisar Dinkin Duniya, musamman na shiyya da na Musulunci, da ‘yan gwagwarmaya, da dukkan duniya ana sa ran nan take za su yi Allah-wadai da wannan aika-aika da kuma daukar matakin gaggawa da hadin gwiwa don tinkarar wannan kasada mai hatsarin gaske wadda ko shakka babu ta nuna yadda zaman lafiya da tsaro a duniya ke cikin wata babbar barazana da ba a taba ganin irinsa ba.”
Iran, ta kuma babu shakka wannan danyen aikin da Isra’ila ta aikata ya samu sahalewar Amurka, don haka a cewar Tehran, Amurka na da hannu a wannan hare haren na Isra’ila.