HausaTv:
2025-05-02@05:01:26 GMT

ICC Na Neman Shaidu Kan Ta’asar Da Aka Aikata A Gabashin DR Congo

Published: 6th, February 2025 GMT

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya na neman shaidu kan halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.

Matakin zai shafi irin ta’asar da aka aikata daga ranar 1 ga watan Janairun 2022 zuwa yau, bisa la’akari da tashe-tashen hankula da aka yi a makonnin baya-bayan nan musamman a birnin Goma – babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

Kotun ta ICC ta ce an jikkata dubban mutane tare da kashe daruruwan mutane a birnin Goma da kewaye.

Daga cikin wadanda harin ya rutsa da su har da fararen hula da dakarun wanzar da zaman lafiya, bayan shafe tsawon watanni ana gwabza fada tsakanin sojojin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango da kungiyar M23 da kawayenta.

Ofishin mai gabatar da kara ya yi kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa, da shaidu, da kungiyoyin kasa da kasa, kungiyoyin farar hula, da su bayar da duk wata shaida da ke hannunsu, dangane da zargin laifukan da dukkan bangarorin suka aikata.

A nata bangaren, DRC tana shirin gabatar da kudiri ga kwamitin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya a wannan Juma’a a birnin Geneva na kasar Switzerland, na neman a gudanar da bincike kan abin da ta kira “gaggarumin take hakkin dan Adam” a birnin Goma.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira

Haka kuma ya nemi kotu da ta bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kuɗi na Naira 200, 500 da  kuma 1000.

Baya ga haka, ya buƙaci a umarci su da su nemi gafara ta hanyar wallafa bayani a manyan jaridu biyu na ƙasa.

Amma a zaman kotu na ranar Litinin, wanda ya shigar da ƙarar da lauyansa ba su halarci zaman kotu ba.

Lauyan da ke kare Emefiele da CBN, Mista Chikelue Amasiani, ya sanar da kotu cewa tun da aka shigar da ƙarar, mai ƙarar da lauyansa ba su nuna wata alama ta son ci gaba da shari’ar ba.

Ya roƙi kotun da ta kori ƙarar.

Mai shari’a Ekwo ya amince da buƙatar kuma ya kori ƙarar, inda ya bayyana cewa mai ƙarar zai iya dawo da ita idan ya shirya yin shari’ar da gaske.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
  • Iran Tace Samar Da Kasar Falasdinu Mai Cikekken Yenci Ba Abin Tattaunawa Bane
  • An Bada Gudummawar Kekunan ga Masu Bukatu Na Musamman A Birnin Kebbi.
  • An Bukaci Masu Yiwa Kasa Hidima Su Yi Amfani Da Kafofin Sadarwa Na Zamani Don Inganta Hadin Kan Kasa.
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira