Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Biya NAHCON Naira Biliyan 4.5 Na Maniyyatan Bana
Published: 6th, February 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta jihar Jigawa ta ce ta mikawa hukumar alhazai ta kasa NAHCON kudaden aikin hajjin maniyyatan jihar na shekarar 2025 kimanin naira biliyan 4.5.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse babban birnin jihar.
Ya ce hukumar ta aika wa NAHCON Naira Biliyan Huda da Miliyan Dari Biyar da Ashirin (4.
Ya bayyana cewa hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta baiwa jihar kujeru 1,809.
A cewarsa, tuni hukumar ta raba kashi 40 cikin 100 ga kananan hukumomin jihar domin gudanar da aikin hajjin bana.
Don haka Labbo ya bukaci Maniyyatan jihar da su gaggauta kammala biyan kudinsu kafin wa’adin da NAHCON ta bayyana, saboda rashin yin haka na iya sa su rasa kujerunsu.
Ya kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba hukumar za ta fara gudanar da taron bita ga maniyyata a cibiyoyin da wasu Malamai suka kebe domin alhazan jihar.
Yayin da yake tsokaci kan masaukin Alhazai, Labbo ya ce hukumar ta samar da masauki na alfarma kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah, domin alhazan jihar su sami damar gudanar da ayyukansu cikin sauki.
Don haka ya bukaci maniyyatan da su ci gaba da bai wa hukumar hadin kai domin cimma burin da ake so.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tun ffarko da hukumar ta sanar da sama da miliyan 8.4 a matsayin kudin aikin Hajjin shekarar 2025 ga maniyyatan jihar.
Shugaban hukumar ya bayyana cewar sun yi taro da jami’an hukumar na shiyoyi, wanda aka gudanar a dakin taro na hukumar da ke Dutse.
Ya yaba da irin goyon baya da kuma kyakkyawar alakar aiki da ake samu a tsakanin mahukuntan hukumar da ko’odinetocin, inda ya yi addu’ar samun dauwamammen hadin gwiwa domin amfanin kowa da kowa da kuma ci gaban jihar.
Ya kuma bayyana cewar sun yi taro da jami’an hukumar na shiyoyi, wanda aka gudanar a dakin taro na hukumar da ke Dutse.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
Ya bayyana cewa, ziyarar da ya kai a tashar ruwa ta PTML da Tin Can na da nufin sanin irin kalubalen da jami’an sa ke fuskanta wurin amfani da sabuwar na’urar zamani domin binciken kayayyakin da ake shigowa da su kasar.
Ya kuma kara gargadin jama’a game da karuwar kwararowar magunguna kasar da ba su da rajista, musamman magungunan inganta jima’i, inda ya yi gargadin cewa irin wadannan abubuwa na da matukar barazana ga kiwon lafiyar jama’a.
Ya yi gargadin cewa, yin amfani da wadannan magungunan ba tare da kulawar likitoci ba zai iya haifar da mummunar illa ga lafiyar jiki, ciki har da haɗarin cututtukan zuciya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp