Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Biya NAHCON Naira Biliyan 4.5 Na Maniyyatan Bana
Published: 6th, February 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta jihar Jigawa ta ce ta mikawa hukumar alhazai ta kasa NAHCON kudaden aikin hajjin maniyyatan jihar na shekarar 2025 kimanin naira biliyan 4.5.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse babban birnin jihar.
Ya ce hukumar ta aika wa NAHCON Naira Biliyan Huda da Miliyan Dari Biyar da Ashirin (4.
Ya bayyana cewa hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta baiwa jihar kujeru 1,809.
A cewarsa, tuni hukumar ta raba kashi 40 cikin 100 ga kananan hukumomin jihar domin gudanar da aikin hajjin bana.
Don haka Labbo ya bukaci Maniyyatan jihar da su gaggauta kammala biyan kudinsu kafin wa’adin da NAHCON ta bayyana, saboda rashin yin haka na iya sa su rasa kujerunsu.
Ya kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba hukumar za ta fara gudanar da taron bita ga maniyyata a cibiyoyin da wasu Malamai suka kebe domin alhazan jihar.
Yayin da yake tsokaci kan masaukin Alhazai, Labbo ya ce hukumar ta samar da masauki na alfarma kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah, domin alhazan jihar su sami damar gudanar da ayyukansu cikin sauki.
Don haka ya bukaci maniyyatan da su ci gaba da bai wa hukumar hadin kai domin cimma burin da ake so.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tun ffarko da hukumar ta sanar da sama da miliyan 8.4 a matsayin kudin aikin Hajjin shekarar 2025 ga maniyyatan jihar.
Shugaban hukumar ya bayyana cewar sun yi taro da jami’an hukumar na shiyoyi, wanda aka gudanar a dakin taro na hukumar da ke Dutse.
Ya yaba da irin goyon baya da kuma kyakkyawar alakar aiki da ake samu a tsakanin mahukuntan hukumar da ko’odinetocin, inda ya yi addu’ar samun dauwamammen hadin gwiwa domin amfanin kowa da kowa da kuma ci gaban jihar.
Ya kuma bayyana cewar sun yi taro da jami’an hukumar na shiyoyi, wanda aka gudanar a dakin taro na hukumar da ke Dutse.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.