Rundunar ƴansanda ta jihar Kwara ta daƙile yunƙurin sace mutane biyu tare da cafke mutum huɗu da ake zargi da hannu a lamarin a ƙananan hukumomin Ifelodun da Baruten.

Kakakin rundunar, Toun Ejire-Adeyemi, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun cafke su ne bayan bin diddigin kiran wayar barazana da wasu mutane suka samu a Ifelodun da Ilesha-Baruba, inda aka buƙace su biya kuɗin fansa har Naira miliyan tara.

Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa Ɗalibin Jami’a Ya Hallaka Kansa Saboda Matsin Rayuwa A Jihar Kwara

Bincike ya kai ga cafke Umar Sanni daga jihar Neja da Dairu Isiaku daga Ifelodun, da kuma Tukur Muhammad da Yahaya Abdullahi, waɗanda suka amsa laifin yin barazana da ƙoƙarin karɓar kuɗin fansa. An gurfanar da su a kotu, kuma an tura su gidan yari domin ci gaba da shair’a.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya

Dakarun rundunar Operation Haɗin Kai sun yi nasarar kashe mayaƙan Boko Haram da ISWAP 24 a wasu sabbin hare-hare da suka ƙaddamar a maɓoyar ’yan ta’addan a yankunan daban-daban a Arewa maso Gabashin Nijeriya.

Kwamandan haɗakar rundunar Operation Haɗin Kai a Arewa Maso Gabas, Janar Abdulsalam Abubakar ya ce an kai samamen ne bayan tattara bayanan sirri.

A cewarsa, an kuma kashe mutum biyar da suke samar wa ’yan ta’addan kayayyakin amfani, a wani kwanton ɓauna da aka yi musu da daddare.

An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu

An gudanar da waɗannan ayyuka ne a tsakanin ranakun 4 zuwa 9 ga watan Yuli a Dajin Sambisa, da Dandalin Timbuktu da kuma Tsaunukan Mandara da ma wasu wuraren daban.

A yayin samamen, rundunar ta ce an yi nasarar ƙwato muggan makamai da dama da babura da kekuna da kayan abinci da kuma kaki da takalman sojoji.

Manjo Janar Abdulsalam ya ce rundunar hadin gwiwa ta bangaren sojin sama, da Civilian Joint Task Force, da na sojojin Nijeriya ne suka gudanar da aikin.

Shi ma Kakakin rundunar ‘Operation Hadin Kai’ Kyaftin Reuben Kovangiya, ya bayar da cikakken bayanin ayyukan a cikin wata sanarwa.

A ci gaba da gudanar da jerin hare-hare na hadin gwiwa a fadin Arewa maso Gabas, sojojin Operation HADIN KAI (OPHK) tare da hadin gwiwar rundunonin sojin sama da hadin gwiwar Civilian Joint Task Force da mafarauta, sun yi nasarar gudanar da samame a kan ’yan ta’addar Boko Haram/ISWAP daga tsakanin 4 zuwa 9 ga Yulin 2025 inda suka kawar da ’yan ta’adda da dama.

A daya daga cikin samamen da aka kai a Platari a ranar 4 ga watan Yulin 2025, yayin da sojojin suka yi kwanton ɓauna, sun far wa ’yan ta’addar JAS/ISWAP da ke kan babura da ke tafiya daga dajin Sambisa zuwa Dandalin Timbuktu.

Nan take aka fatattaki ‘yan ta’addan ta hanyar buɗe musu wuta, lamarin da ya kai ga halaka ‘yan ta’adda 3.

Kazalika, bayan samun bayanan sirri kan zirga-zirgar ’yan tada kayar bayan a kewayen yankin Komala, sojoji sun sake yi wa ’yan ta’adda kwanton ɓauna, inda suka kashe wani mayakin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama mai garkuwa da mutane da bindigogi
  • HKI Ta Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Kudancin Kasar Lebanon
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya
  •  HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi
  • Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
  • Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda
  • ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja
  • HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya
  • Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda