Rundunar ƴansanda ta jihar Kwara ta daƙile yunƙurin sace mutane biyu tare da cafke mutum huɗu da ake zargi da hannu a lamarin a ƙananan hukumomin Ifelodun da Baruten.

Kakakin rundunar, Toun Ejire-Adeyemi, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun cafke su ne bayan bin diddigin kiran wayar barazana da wasu mutane suka samu a Ifelodun da Ilesha-Baruba, inda aka buƙace su biya kuɗin fansa har Naira miliyan tara.

Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa Ɗalibin Jami’a Ya Hallaka Kansa Saboda Matsin Rayuwa A Jihar Kwara

Bincike ya kai ga cafke Umar Sanni daga jihar Neja da Dairu Isiaku daga Ifelodun, da kuma Tukur Muhammad da Yahaya Abdullahi, waɗanda suka amsa laifin yin barazana da ƙoƙarin karɓar kuɗin fansa. An gurfanar da su a kotu, kuma an tura su gidan yari domin ci gaba da shair’a.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno

Dakarun Operation Haɗin Kai da ke Arewa maso Gabas, sun ɗakile wani sabon hari da mayaƙan Boko Haram suka kai a Jihar Borno.

Sun kai harin ne yankunan Konduga, Bama da Gwoza.

Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000

’Yan ta’addan sun yi yunƙurin tarwatsa gadar da ke kan hanyar Marte zuwa Dikwa ta hanyar dasa bama-bamai.

Amma sojoji sun gano abubuwan fashewa guda 17 da suka dasa a ƙarƙashin gadar kuma suka cire su.

A yayin daƙile harin, sojoji sun kashe ’yan ta’addan Boko Haram guda tara, sannan sun ƙwato bindigogi ciki har da AK-47 da bindigar PKT.

Kakakin rundunar sojin a Maiduguri, Kyaftin Reuben Kovangiya, ya ce dakarun na ci gaba da kai farmaki da sanya ido kan ayyukan ‘yan ta’addan a yankin.

Ya ce wannan nasarar na nuna cewa sojoji sun ƙudiri aniyar hana ’yan Boko Haram da ISWAP aikata ta’addanci.

Rundunar sojin ta roƙi jama’a da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar bayar da rahoton motsin duk wani mutum da suke zargi yana da alaƙa da ’yan ta’adda ga jami’an tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu
  • Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar