Aminiya:
2025-08-01@16:12:16 GMT

Matar aure kashe dan kishiyarta da tafasasshen ruwa

Published: 6th, February 2025 GMT

An kama wata matar aure bisa zargin ta da kashe dan kishiyarta ta hanyar zuwa masa  tafasasshen ruwa a kaciyarsa a garin Dawakin Tofa da ke Jihar Kano.

’Yan sanda a Jihar Kano na zargin matar ta je ta dauki yaron ne a wurin kakarsa, ida ake kula da shi bayan an yi masa kaciya, kasancewar mahaifiyarsa da mahaifin sun rabu.

Bayanai sun nuna cewa duk da cewa kakar ta ki amincewa, amma sai da matar ta nace ta dauki yaron da cewa za ta kula da shi, bayan nan ne kuma sanya masa tafasasshen ruwa a gaban nasa, maimakon ruwan dumi.

Duk da raunin da tafasasshen ruwan ya yi  masa kuma, sai aka kai shi wurin mai maganin gargajiya maimakon asibiti, inda bayan kwana uku rai ya yi halinsa.

HOTUNA: Yadda gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Kano Ɗan firamare ya je makaranta da bindiga yana barazanar harbe ɗalibai An kashe wa ma’aurata ’ya’yansu uku an ɓoye gawarsu a firinji

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa matar tana tsare ana mata tambayoyi kafin a gurfanar da ita a gaban kuliya.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

GORON JUMA’A 01-07-2025

Tarihin dan’adam ya nuna yadda ƙabilu daban-daban, ke nuna ƙin amincewa da auratayya ta haɗin gambiza a tsakanin ƴaƴansu da wasu ƴan ƙabilar da ba tasu ba. Hatta a cikin ƙabila daya ana samun wannan nuna wariya, tsakanin dangi, ko masu hali da talakawa. Hatta a tsakanin addini daya, bambancin aƙida ko fahimta na sa a hana masoya aure, ko da kuwa sun cancanci kasancewa tare.

Kodayake zamani na sauyawa, ilimi na ƙara yawa, mutane na dada samun wayewa kan ƴancin su, amma a wurare da dama aure daga wata ƙabila zuwa wata, abin kyama ne. Wasu na son ko da za a auro daga wata ƙabila to, ya kasance ba auren fari ba ne. Ko kuma ya kasance mai bin addini daya da su ne. Mutane suna son ƙabilar su ta ƙara yawa, al’adarsu da tarbiyyar su ta cigaba da wanzuwa, don kada tarihin su da harshen su na gado ya ɓace. Sai dai hakan na nuna ƙuntatawa ga matasa da wadanda suke son juna, yana tauye musu ƴanci da haƙƙoainsu.

Sunana Haj. Binta Umar Ahmad, daga Limawa:

Gaskiya ne cewa wasu ƙabilu ko al’ummomi, na iya samun abubuwan da suka fi so ko al’adu da ke tasiri a kan yadda ake gudanar da aure. Wadannan na iya kasancewa daga ƙarfafa aure a cikin ƙabilar zuwa samun takamaiman al’adu ko tsammanin al’adu. Wadannan al’adu sau da yawa suna fitowa daga sha’awar kiyaye gadon al’adu, kula da haɗin kan al’umma, ko kuma tsayawa kan imanin addini. ɗuk da haka, yana da muhimmanci a tuna cewa zaɓuɓɓuka da ra’ayoyi na mutum na iya bambanta sosai a cikin kowace ƙungiya.

Amfanin su ne; yin aure a cikin ƙabila daya yana taimakawa wajen kiyaye al’adu, harsuna, da ayyuka, tabbatar da isar da su ga tsararraki masu zuwa. Yana iya ƙarfafa haɗin gwiwar al’umma da haifar da jin daɗin zama a tsakanin ƴan ƙabila daya. Ma’aurata daga ƙabila daya sau da yawa suna da dabi’u, da al’adu iri daya, wanda hakan zai iya haifar da raguwar rikice-rikice a cikin aure. Iyalai da al’ummomi na iya samar da hanyoyin sadarwa masu ƙarfi ga ma’aurata, tare da taimaka musu su magance ƙalubale tare.

Kuma matsalolin sune ƙuntata aure zuwa cikin rukuni na iya iyakance zaɓi na sirri da damar soyayya da abota. Wannan al’ada na iya haɓaka tunanin ‘mu da su’, wanda zai haifar da wariya ko kyama ga wadanda suka fito daga wurare daban-daban. Sannan yana kawo rigingimun Al’adu, aure tsakanin ƙabilu na iya haifar da rashin fahimta a wasu lokuta ko rigima saboda bambancin al’adu da abin da ake tsammani.

Mutanen da suka yi aure a wajen ƙungiyarsu na iya fuskantar kyama ko rashin yarda daga al’ummarsu. Wadannan abubuwan na iya bambanta sosai dangane da ƙayyadaddun ƙabila da mahallin da suke rayuwa.

Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To, haƙiƙa yin hakan kuskure ne domin shi arziƙi nufi ne na Allah, kuma wasu sai bayan auren ma suke samun arziƙin, amma ba laifi bane don iyaye sun zaɓawa ƴaƴan su mata miji domin hakan zai taimaka wajen samun nagari. To, batun ƙabilanci sam-sam bai dace ba, domin ba a duban ƙabila wajen bada aure ko neman aure, ana duba addini ne, dabi’a dama nasaba.

Amma ba laifi bane iyaye su taya ƴaƴan su, zaban mijin nagari. Eh tabbas akwai hakan yana haifar kiyayya a tsakanin al’umma ko ƙabila, wanda ka iya jawo zaman doya da manja, a ɓangaren zaɓan mijin mai hali kuma irin wannan dabi’a tana rage darajar iyaye dama gidan a idon duniya. To, shawara ta a nan ita ce wajen zaɓen mijin a fifita zaɓen mai addini, dabi’a mai kyau dama nasaba akan ƙabilanci ko mai abun hannu, su kuma su dage wajen yi wa ƴaƴan su addu’ar samun mazaje nagari ba wai masu dukiya kadai ba, domin bawa Allah zaɓi zai taimaka wajen samun nagari.

Sunana Rahma Adamu Ahmad, daga Jihar Kaduna:

Hakan yana nuna wariya da rashin adalci. Auren soyayya da fahimta ya fi inganci fiye da wanda aka gina kan ƙabilanci ko dukiya. Amfani. A wasu lokuta iyaye na kallon tsaron ƴaƴansu ne da bin wannan hanya, musamman ta fuskar kuɗi. Rashin amfani: Yana hana soyayya ta gaskiya, yana hana haɗin kai da gina al’umma mai ƙarko. Kiyayya da rashin jituwa tsakanin ƙabilu,

Hana cigaban al’umma ta hanyar hada jini, Tilasta wa yara auren da ba sa so, wanda ke janyo matsaloli cikin gida, Rasa damar dogaro da kai idan an hana matasa fita neman arziƙi. A bawa yara ƴanci wajen zaɓen abokin rayuwa, matuƙar yana da tarbiyya da nagarta. A riƙa duba halayya da imani, ba ƙabila ko dukiya ba. Kuma a koya wa yara darajar aiki da nemowa da kansu.

Sunana Comr, Nr. Ibrahim Lawan Stk:

dalilin da ya sa wasu ƙabilun ba sa barin auratayya a tsakankaninsu da wasu ƙabilun shi ne; mafi akasari saboda bambamce-bambamce na addini da al’ada da kuma yare tare da riƙe sirrin junansu, haka kuma sun zaɓawa yaransu masu kuɗi ne domin kaucewa talauci ga yaran nasu mata dama jikokinsu, hakan tasa ba sa yadda yaransu mata su auri talakawan cikinsu.

Sannan ba sa barin talakawan cikin nasu su auri wasu matan da ba ƙabilinsu bane ba. Sannan sukan alaƙanta hakan da sabo ko sabawa al’ada da kuma tarihi ta yadda talakawan cikinsu za su kasance masu yi wa dokokin ƙabilar su biyayya don auren mata ƴaƴan talakawa dake a cikin ƙabilarsu.

Amfanin yin hakan zai haifar da danƙon zumunci da kuma ɗorewar al’ada ta ƙabilancinsu. Sannan sai tabbatar da ɗorewar cigaban ƙabila, haka ma rashin amfanin hakan zai sa talakawan ƙabilar su cigaba da kasancewa cikin talauci sannan hakan zai iya haifar da rashin jituwa, rashin zaman lafiya da haɗin kai tare da rashin fahimta a tsakanin ƙabilu daban-daban. Matsalolin da ka iya samuwa sun hada da; rashin samun cigaba, rashin chanzawar matsayi, rashin tsaro, rashin zaman lafiya, rikicin ƙabilanci, cin amanar juna, rashin aikin yi, talauci da fadawa cikin mawuyacin hali tare da sarewa rayuwa ko fadawa amfani da miyagun kwayoyi da safararsu.

Shawarar ta hada da su tuna cewa babu abin da hakan zai haifar face rashin zaman lafiya da cigaba sannan su kasance masu tunanin cewa duka mutanen duniya daya ne babu wanda ya fi wani sai mafi tsoran Allah da kuma mafi yin biyayya a gare shi da kuma dokokinsa, su kuma sani cewa Allah ne mai bada arziƙi da talauci kasancewar mutum a cikin daya jarabawar sa ce, kuma ni’imar sa ce don zai iya bawa mutum arziƙi ya kuma kwace ya bawa mutum talauci. Haka kuma zai iya bawa mutum talauci, ya kuma kwace ya bashi arziƙi, duk hakan cikin ni’imominsane.

Sunana Princess Fatima daga Gomben Najeria:

Abin sai godiya wanda abu ne ada ana yin shi dan gudun rasa yayaye, da kuma gaba tsakanin ƙabilu. Amma a yanzu ya zamo, kamar kyama ma ake yi wanda sam bai dace ba. Iyaye suna da damar zaɓawa yaransu mata ko mazaje, amma ba ta hanyar tilastawa ba, su kafe lallai sai mai kuɗi zai auri ƴar su ko sarauta ko dai abu madangancin dukiya, wasu sun kyamaci talauci duk da talauci kam wallahi abun gudu ne shi talakan ma ya yi arziƙi aka kira talauci sai ya juya dan tsoron kar ta sake biyo shi, yawanci zuriya in dai an ga wani ya yi dukiya to, fa! fatansu kawai kar ya auro wata a waje wai da na waje ya ci gwara na ciki ya ci ko cikin ɓacin rai, Allah ya kyauta.

Abu ne mara kyau abar kowa ya zaɓi rabonshi aure na Allah ne mai kuɗi da talaka duk bayin Allah ne, haka za ka iya aurawa ƴar ka mai kuɗin ya talauce ko ka aura mata talaka ya yi arziƙi. Amfaninshi kam shi ne haɗin zumunci kawai bayan shi komai sai kwadayi da burin komai su kar ya fita ya ƙare a cikin gida su ya su. Matsaloli kam ai barkatai ne sai dai a faɗi kadan, kamar zaman dole da-na-sani da tsayiwar zuci kar arziƙin ya mulmulce. Haka auren ƙabilu wani lokacin da-na-sani ne dan al’ada ba ta zo daya ba ra’ayi ba dole ya zamo daya ba, wani lokacin kuma haɗin auren tsakani kan iya kawo ƙarin zaman lafiya ga a’lumma da haɗin kai. ɓangaren auren masu kuɗi buri da kwadayi, ta auratayya tsakanin ƙabilu kuma zaman lafiya ko akasinsa.

Shawara kowa ya san daidai a bita kawai a zauna lafiya, a kuma daina kyamatar talaka, dan shi kan shi talaka ba ya son talauci, sunanan kyamatar ƙabila ko jahiltarsu ba kyau indai akwai fahimtar juna to, magana ta ƙare.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), JIhar Kano:

Son kai ne kawai. Rashin amfanin hakan yana rage ƙaruwar zumunci da kawo haɗin kai cikin al umma. Amfanin hakan kuma zai ƙara yawan dangi cikin al’umma. Kadan daga cikin irin matsalolin akwai haddasa gaba da kin yarda da juna da kuma haddasa fadace-fadace. Shawarata a nan ita ce su daina, domin ko irin taken da ake wa nahiyar mu ta Africa da kuma ita kanta ƙasata wato Nigeria shi ne ‘Uwa daya Uba daya’ mu daure mu cire son zuciya da son kai musamman mu ƴan yankin arewa mafiya yawanmu Hausa Fulani ne kuma musulmi. Allah kasa mudace.

Sunana Hafsat Sa’eed daga Jihar Naija:

Shawarata a nan ita ce, yin magana tare da abokin tarayya game da bambance-bambancen al’adu, gudun tsammanin rikice-rikice masu yuwuwa. Su kasance da sha’awar al’adun abokin tarayya da al’adunsu. Yin tambayoyi ko karanta littattafai ko kallon shirye-shiryen bidiyo, da ƙoƙarin koyo gwargwadon iyawa domin samun zaman lafiya da juna. Wannan yana taimakawa wajen cike giɓin al’adu, ƙarfafawa iyalansu gwiwa don sanin juna, wannan yana taimakawa wajen haɓaka fahimta da yarda. Su yi haƙuri da junansu ya yin da suke da bambancin al’adu, dabi’u, da sauran abubuwa daban-daban.

Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor) daga kano:

Allah daya, gari bamban.

Gaskiya wannan abin na su sai addu’a, ko da yake al’adar su ce ko to ai zabin Allah dai shi ne gaba da komai da fatan samun nagari ba kuɗin ba. Ai babu wani amfanin bin wannan tsarin nasu sam ai bin su sai su kam wallahi. Matsaloli sosai za su sa yaransu fadawa kungiyoyin asiri da fashi da makami, garkuwa da mutane da sauransu, Allah ya kyauta amin. Su yi haƙuri da abin da Allah ya ba su mai kuɗin ko talaka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi
  • GORON JUMA’A 01-07-2025
  • Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar