Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@23:03:37 GMT

PCN Ta Kai Ziyara Ga Hukumar Samarda Magunguna Ta Jihar Kano

Published: 6th, February 2025 GMT

PCN Ta Kai Ziyara Ga Hukumar Samarda Magunguna Ta Jihar Kano

Hukumar Kula da Magunguna ta Najeriya (PCN) ofishin Kano ta kai ziyarar gani da ido ga hukumar samar da magunguna ta jihar Kano (DMCSA).

 

Wannan ziyarar alama ce ta farkon tsarin ba da izini ga DMCSA don zama cibiyar rarraba magunguna ta mega da cibiyar bada horo.

 

Jami’ar Jihar Kano mai kula da ofishin PCN Kano Pharmacist Hasiya Abubakar Ladan ce ta jagoranci tawagar da suka kai ziyarar.

 

Wannan ziyarar wani mafari ne na tantancewa da wata tawagar kwararru daga hedikwatar PCN ta kasa da ke Abuja.

 

Ta bayyana cewa ziyarar na da nufin tantance yadda DMCSA ke bin ka’idoji, don ba da Takaddar Rijistar wuraren sayarda magunguna.

 

Pharmacist Ladan ta yabawa shugabannin DMCSA bisa yadda suke tafiyar da ayyukan kungiyar yadda ya kamata tare da nuna gamsuwa da matakin da hukumar ta dauka.

 

Darakta Janar na DMCSA Pharmacist Gali Sule, ya tarbi tawagar inda ya zagaya da su a rumbunan adana kayayyaki.

 

Ya bayyana cewa hukumar ta dakatar da samar da magunguna domin inganta sashin sarrafa magunguna kamar yadda PCN da NAFDAC suka bada shawara.

 

Pharmacist Sule ta godewa tawagar bisa ziyarar da suka kai tare da ba su tabbacin hadin kan DMCSA a duk lokacin da ake gudanar da aikin tantancewa.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tantancewa

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin dindindin na kasar Sin a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ko IAEA Li Song, ya ce kasarsa na matukar Allah wadai da harin Isra’ila kan cibiyoyin sarrafa nukiliyar Iran da ake amfani da su domin ayyukan zaman lafiya.

Li Song, ya bayyana hakan ne a jiya Juma’a, yayin taron manyan jami’an majalisar gudanarwar hukumar ta IAEA, game da batun hare-haren da Isra’ila ta kaddamar kan cibiyoyin sarrafa nukiliyar Iran. Ya ce, har kullum Sin na mayar da hankali ga zakulo matakan wanzar da zaman lafiya, dangane da batun nukiliyar Iran ta hanyoyin siyasa da diflomasiyya, tana kuma adawa da kakaba takunkumai ba bisa ka’ida ba daga bangare guda. Har ila yau, Sin za ta ci gaba da tattaunawa ta kut-da-kut da dukkanin sassan da batun ya shafa, tare da shawo kan batutuwan gaggawa dake gaban majalisar gudanarwar hukumar ta IAEA. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya