Duniya Na Ci Gaba Da Mayar Wa Da Donald Trump Martani Akan Gaza
Published: 6th, February 2025 GMT
Kasashen larabawa masu kawance da Amurka sun kasance a sahun gaba wajen mayarwa da shugaban kasar Amurkan martani, bayan da ya bayyana cewa kasarsa za ta shimfida ikonta a Gaza, bayan fitar da Falasdinawa da Gaza.
Gabanin wannan sanarwar ta Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa ya tuntubi kasashen Jordan da Masar masu makwabtaka da Falasdinu da su karbi bakuncin mutanen Gaza na wani lokaci har zuwa sa’adda za a gyara wajen.
Masar da Jordan sun yi watsi da wannan shirin da suke dauka a matsayin wata dabara ce ta fitar da Falasdinawa daga cikin kasarsu, da maye gurbinsu da yahudawa ‘yan share wuri zauna.
A wani bayani da kungiyar hadin kan Larabawa ta fitar ta bayyana cewa; Abinda Trump din ya fada yana da tayar da hankali, kuma yin kira ne ga hargitsa yankin.
Kungiyar mai kasashe mambobi 22 ta kuma kara da cewa, wannan shawara da Trump ya fito da ita, tana cin karo da dokokin kasa da kasa.
Ita ma kungiyar kasashen musulmi ta ( OIC) da take wakiltar musulmin duniya miliyan 1.5, ta ce za ta ki amincewa da wannan shawarar wacce take son sauya tsarin zamantakewa na wannan yankin.
Wasu daga cikin kasashen wannan yankin abokan Amurka da su ka yi watsi da shirin na Trump na korar Falasdinawa daga Gaza sun hada Saudiyya, Jordan, Masar, Katar da Hadaddiyar Daular Larabawa, sai kuma Turkiya.
Ita ma MDD ta bayyana cewa hanyar kawo karshen batun Falasdinu shi ne abinda ta kira; Kafa kasashe biyu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,