Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Nemi Maniyyata Su Kammala Biyan Kudinsu Kafin Cikar Wa’adi.
Published: 5th, February 2025 GMT
Yayin da Hukumar Kula da Hajji ta Kasa ta kara wa’adin biyan kudin Hajjin bana zuwa ranar 10 ga watan Fabrairu, Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna ta umarci dukkan ofisoshin da suke alhakin yin rajista su tabbatar da an yi wa duk masu sha’awar tafiya Hajji rajista kafin ƙarshen wa’adin da aka ƙara.
Shugaban Hukumar, Malam Salihu Abubakar, ya kuma yi kira ga dukkan maniyyatan da ba su kammala biyan kuɗinsu ba da su gaggauta yin hakan.
Ya jaddada cewa ba za a ƙara wa’adin bayan ranar 10 ga Fabrairu ba, don haka ya bukaci maniyyata su yi amfani da wannan damar su kammala rijistarsu kafin ko zuwa Litinin, 10 ga Fabrairu, 2025.
Rel/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Biyan Cikar Hukumar Jihar Maniyyata Wa adin Rajista
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa sabon Sarkin Moro’a, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo sandar mulki, a wani biki da aka gudanar a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura.
Gwamna Sani, ya bayyana cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen zaman lafiya, haɗin kai da kuma ci gaban al’umma.
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a BinuwaiYa ce gwamnatinsa na bai wa sarakunan gargajiya cikakken goyon baya saboda irin rawar da suke takawa a harkar mulki da ci gaban jama’a.
“Mun jajirce wajen haɗa kan al’umma a faɗin Jihar Kaduna, ba tare da nuna bambanci ba.
“Yanzu Jihar Kaduna ta fi samun tsaro da kwanciyar hankali fiye da da. Wannan nasara ta samuwa ne sakamakon gudunmawar sarakunan gargajiya,” in ji Gwamnan.
Ya kuma buƙaci al’ummar jihar da su zauna lafiya da juna tare da yin aiki tare domin ciyar da jihar gaba.
Haka kuma, ya roƙi sarakunan da su ci gaba da jagorantar al’ummominsu cikin adalci da riƙon amana.
Bikin naɗin sarautar ya samu halartar baƙi daga sassa daban-daban, bayan rasuwar tsohon Sarkin Moro’a, Malam Tagwai Sambo, wanda ya rasu ranar 14 ga watan Yuni 2024.
Tsohon Sarkin ya rasu yana da shekaru 88, bayan mulkin shekaru 58.
Sabon Sarkin, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo, ya gode wa gwamnati da al’ummar Moro’a bisa amincewar da suka yi masa.
Ya yi alƙawarin mulki cikin gaskiya da riƙon amana tare da bin doka da oda.
“Zamu haɗa kai da majalisar masarauta da kuma ɗaukacin al’umma domin tafiyar da wannan mulki yadda ya kamata,” in ji shi.