Kungiyar Hizbullah ta fitar da wani bayani a jiya Talata da ta yi Allawadai da takuhkumin da kasar Australia ta kakaba wa babban sakatarenta Sheikh Na’im Kassim.

Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kunshi cewa; Matakin, yana sake nuni ne da hakikanin fuskar wannan kasa da a kowace rana take tabbatar da cewa, ita makami a hannun Amurka da Isra’ila.

Hizbullah ta kuma bayyana matakin da cewa na zalunci ne wanda bai jingina da kowane irin dalili na shari’a da halayyar kwarai ba, yana nuni ne kai tsaye da cewa; Suna goyon bayan HKI ne da kuma kare laifukan da take tafkawa da ta’addancinta, tare da yin kira cewa kamata a yi ace kasar ta Australia da ta dauki matakai ne na ladabtarwa akan ‘yan sahayoniya makasa, ta kuma kasance a tare da wadanda ake zalunta a Lebanon da Falasdinu.

Bayanin ya kuma ce: Duk duniya ta ga yadda abokan gaba ‘yan sahayoniya su ka rika yin kisan kiyashi da laifukan yaki akan wadanda ba su ji ba su gani ba a Gaza da kuma Lebanon, don haka duniyar ta san wanene dan ta’adda na hakika, da kuma wanda yake yin kisan kiyashi da tafka laifukan yaki.

Haka nan kuma bayanin ya ce, duniya ta kuma san su wanene suke bayar da kariya ga ‘yan mamaya a siyasance, yake kuma yin tarayya da ita a kisan kiyashin da take yi.

Sai dai kungiyar ta Hizbullah ta ce, wannan matakin babu yadda zai yi tasiri akan ‘yan gwgawarmaya a cikin Lebanon, ko kuma akan matakan da Hzibullah take dauka na kare kasa da al’umma da kuma kasancewa a tare da al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi

Kakakin gwamnatin JMI ta bayyana cewa a dai-dai lokacinda Amurka ta kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar , babu wata tattaunawa da Amurka nan kusa, duk tare da cewa Amurkawan sun bayyana cewa za’a ci gaba da shi.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin gwamnatin kasar Iran Malama Fatimah Muhajirani tana fadar haka a jiya Talata, ta kuma kara da cewa, babu wata rana da aka sanya na tattaunawa da Amurka kuma mai yuwa babu wata tattaunawa da ita nan kusa.

Fatima tana maida martani ne ga wata sanarwan da gwamnatin kasar Amurka ta bayara na, na cewa nan kusa zasu sake farfado da tattaunawa da JMI.  Tehran dai ta bayyana cewa bata bukatar wani tattaunawa da Amurka kuma bayan hare-haren da ta kai kan cibiyoyin nukliyar kasar guda 3 a dai dai lokacinda HKI ta fadawa kasar da yaki tare da amincewarta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • ‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
  •  Muhsin Rizai: Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Bayar Da Umarni  Da Jagorantar Yakin “Wa’adussadiq 3”
  •  Sheikh Na’im Kassim:  Ba Za Mu Taba Mika Makamanmu Ga Makiya Ba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda
  • Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi
  •  Na’im Kassim: Mamaya Tana Da Ranar Da Za Ta Zo Karshe
  • Isra’ila na neman ƙulla hulɗa da Siriya da Lebanon
  • Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19