Kungiyar Hizbullah ta fitar da wani bayani a jiya Talata da ta yi Allawadai da takuhkumin da kasar Australia ta kakaba wa babban sakatarenta Sheikh Na’im Kassim.

Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kunshi cewa; Matakin, yana sake nuni ne da hakikanin fuskar wannan kasa da a kowace rana take tabbatar da cewa, ita makami a hannun Amurka da Isra’ila.

Hizbullah ta kuma bayyana matakin da cewa na zalunci ne wanda bai jingina da kowane irin dalili na shari’a da halayyar kwarai ba, yana nuni ne kai tsaye da cewa; Suna goyon bayan HKI ne da kuma kare laifukan da take tafkawa da ta’addancinta, tare da yin kira cewa kamata a yi ace kasar ta Australia da ta dauki matakai ne na ladabtarwa akan ‘yan sahayoniya makasa, ta kuma kasance a tare da wadanda ake zalunta a Lebanon da Falasdinu.

Bayanin ya kuma ce: Duk duniya ta ga yadda abokan gaba ‘yan sahayoniya su ka rika yin kisan kiyashi da laifukan yaki akan wadanda ba su ji ba su gani ba a Gaza da kuma Lebanon, don haka duniyar ta san wanene dan ta’adda na hakika, da kuma wanda yake yin kisan kiyashi da tafka laifukan yaki.

Haka nan kuma bayanin ya ce, duniya ta kuma san su wanene suke bayar da kariya ga ‘yan mamaya a siyasance, yake kuma yin tarayya da ita a kisan kiyashin da take yi.

Sai dai kungiyar ta Hizbullah ta ce, wannan matakin babu yadda zai yi tasiri akan ‘yan gwgawarmaya a cikin Lebanon, ko kuma akan matakan da Hzibullah take dauka na kare kasa da al’umma da kuma kasancewa a tare da al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza

Rahotannin da suke fitowa daga Gaza sun ce, fiye da Falasdinawa 35 ne su ka yi shahada daga Safiyar yau Laraba zuwa  tsakiyar rana,sanadiyyar hare-haren da HKI take kai wa.

Hakan tana faruwa ne a daidai lokacin da ma’aikatar  kiwon lafiya a Gaza ta yi gargadi akan cewa asibitocin yankin sun kusa daina aiki baki daya.

Tashar talabijin din ‘aljazira’ ta kasar Qatar ta ce,adadin wadanda su ka yi shahada har zuwa marecen yau sun kai 51,38 daga cikinsu a cikin birnin Gaza kadai.

A gefe daya rahoton tashar talbijin din ta ‘aljazira’ ya  bayyana cewa; HKI ta yanke hanyoyin sadarrwa na “Internet’ a fadin Gaza, haka nan kuma ta hana hukumar lafiya ta duniya ( w.h.o) shigar da makamashi cikin asibitocin yankin.

Ma’aikatar kiwon lafiya a Gazan ta kuma ce, matukar ba a bari aka shigar da makamashi cikin asibitocin yankin ba, to komai zai tsaya.

A can yankin yammacin kogin Jordan kuwa, sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinawa 40 a garin ‘Assir” a yau Laraba kadai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila September 17, 2025 Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta September 17, 2025 Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata