Masu Fama Da Cutar Daji Sun Bukaci Gwamnatin Kano Basu Tallafi
Published: 5th, February 2025 GMT
Kungiyar masu fama da cutar daji ta Najeriya reshen jihar Kano, ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta bullo da tallafin kula da cutar a dukkan asibitocin gwamnati.
Shugaban kungiyar Salisu Yusuf ne ya yi wannan kira a yayin wani taron manema labarai na bikin ranar cutar Daji ta duniya tta shekarar 025.
Ya bukaci gwamnati da ta hada gwajin cutar Kansa, da jiyya, da kula da lafiyar jiki a cikin shirinta na ba da tallafin iwon lafiya.
Acewarsa matakin zai rage wa majinyata matsalar kudi, musamman wadanda suka fito daga iyalai masu karamin karfi.
Bugu da kari, kungiyar ta bukaci da a saka masu fama da cutar ta Daji da wadanda suka warke daga cutar a cikin shirin nan na Abba Care da aka kaddamar kwanan nan, wanda ke da nufin tallafa wa mutane masu raunu su 300,000.
Salisu Yusuf ya jaddada cewa cutar Kansa ta kasance babbar lalurar da ke bukatar kulawa cikin gaggawa. “Yawancin mutane na kokawa dangane da biyan kuɗin tantance masu dauke da cutar, da kudaden cigaba da samun kula da karbar magani idan aka gano suna dauke da cutar.
Kungiyar ta masu fama da cutar daji ta Najeriya ta yabawa kokarin gwamnatin jihar na inganta fannin kiwon lafiya, tare da yin kira ga masu hannu da shuni, da kungiyoyi masu zaman kansu, da cibiyoyin kiwon lafiya masu zaman kansu, da su tallafawa shirin kula da cutar Daji a Kano.
Ta jaddada kudirinta na bayar da shawarwarin sauye-sauyen tsarin da ke ba masu fama da cutar Kansa fifiko a Kano, ta hanyar wayar da kan jama’a da shirye-shiryen gano cutar da wuri.
Taken ranar Ciwon Daji ta Duniya na 2025, “United by Unique,” yana nuna mahimmancin aikin gamayya wajen yaƙar cutar Kansa.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ranar Cutar Daji Ta Duniya masu fama da cutar da cutar Daji cutar Kansa da cutar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
Gwamnatin tarayya ta umarci hukumar shirya jarrabawar WAEC da NECO da su fara amfani da cikakken tsarin amfani da Komfuta (CBT) ga dukkan jarabawar su nan da shekarar 2026. Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ne ya bayar da wannan umarnin a ranar Litinin yayin ziyara da kuma duba yadda ake gudanar da gwaje-gwaje na CBT a cibiyoyin Bwari da kuma duba ɗakin gwajin jarrabawa JAMB a kwamfuta.
Alausa ya bayyana cewa, daga watan Mayu ko Yuni na 2026, duka ɓangarorin tambayoyin da aka saba na WAEC da NECO, na rubutu da na gwaje-gwaje, za su kasance a komfuta gaba ɗaya. Ya ƙara da cewa wannan matakin na daga cikin manufar gwamnatin na magance matsalar satar jarabawa.
Gwamnatin Kano Ta Biyawa Ɗalibai 119,903 Kudin Jarrabawar NECO Da NBAIS WAEC Ta Kwace Lasisin Makarantu 574 Sakamakon Satar AmsaMinistan ya kuma sanar da cewa an kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Daraktan JAMB, Prof. Ishaq Oloyede, wanda zai duba tsarin jarabawar Nijeriya gaba ɗaya, inda aka ce sakamakon binciken zai fito nan da ƙarshen watan gobe. Alausa ya yaba da ingancin gudanar da jarabawar UTME ta 2025 da JAMB, wanda ya bayyana a matsayin “matsayi na duniya” kuma yana cika ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.
A cikin jawabinsa, Oloyede ya bayyana cewa UTME ta 2025 tana ɗaya daga cikin mafi kyawun jarabawar da aka taɓa gudanarwa, inda ya kuma bayyana cewa duk wani zargin rashin dacewar cibiyoyin jarabawa yana buƙatar hujja mai ƙarfi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp