An Kara Wa’adin Yin Rajistan Aikin Hajjin 2025
Published: 5th, February 2025 GMT
Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON ta sanar da a ci gaba da yi wa maniyyata rajista har zuwa ranar Litinin 10 ga watan Fabrairu, 2025.
A daren Talata 4 ga watan ne hukumar ta amince da kara lokacin a taron da ta yi da shugabannin hukumomin alhazai na jihohi.
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Jin Dadin Alhazzai ta Jihar Kaduna Yunusa Mohammed Abdullahi ya fitar, ya ce shugaban hukumar Malam Salihu S.
Ya ce wannan ita ce dama ta ƙarshe da suka nema a wajen taron da suka yi da NAHCON.
Kudin kujera a bana dai ya kama Naira miliyan takwas da dubu dari hudu da hamsin da biyar, da dari shida da tamanin da biyar, da kobo hamsin da tara(8, 457, 685.59).
Safiyah Abdulkadir
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Wa adin Rajista
এছাড়াও পড়ুন:
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.
“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp