HausaTv:
2025-07-31@17:51:22 GMT

Kasashen Gabashi Da Kudancin Afrika Zasuyi Taro Kan Rikicin Gabashin Kongo

Published: 4th, February 2025 GMT

Kasar Kenya mai rike da shugabancin kungiyar kasashen gabashin Afirka ta EAC, ta sanar cewa za’a gudanar da wani taron hadin gwiwa da kungiyar raya kasashen yankin kudancin Afirka ta SADC a ranar Juma’a a Dar es Salaam, babban birnin kasar Tanzania.

Taron na kwanani biyu zai samu halartar shugabannin kasashen Rwanda da Kongo, Paul Kagame da Félix Tshisekedi.

Al’amura sun dagule a yankin na gabshin Kongo bayan harin da ‘yan tawayen M23 – da Rwanda ke marawa baya suka kai a Goma, babban birnin Kivu ta Arewa, a makon jiya, da kuma fadan baya-bayan nan a Kudancin Kivu.

A cikin ‘yan kwanakin nan, kungiyoyin biyu da ke da ra’ayi daban-daban kan yadda za a warware rikicin, sun bayyana fatan shirya taron hadin gwiwa na gaggawa domin daidaita matsayarsu da kuma kaucewa hadarin da ke tattare da rikicin yankin. “

Manufar wannan babban taron it ace ci gaba da kokarin “sake tuntuba ta diflomasiyya don kawo karshen tarzomar” a gabashin DRC.

A wani labarin kuma Kwamitin Kare Hakkokin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya zai yi taro cikin gaggawa a ranar Juma’a domin duba rikicin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango da kuma tasirinsa kan ‘yancin bil’adama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

Yau Litinin, an gudanar da taron dandalin tattaunawar neman sabon tunani na asali na 2025 a birnin Hangzhou dake lardin Zhejiang. Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin, Li Shulei, ya halarci taron tare da gabatar da jawabi.

Mahalarta taron sun bayyana cewa, ya kamata mu ci gaba da sa kaimi ga yin gyare-gyare da kirkire-kirkire yayin bunkasa al’adun gargajiya na kasar Sin, da kuma nuna kimar kasar Sin da karfin wayewar kai da al’adu. A sa’i daya kuma, kamata ya yi a horar da manyan kwararru na al’adu, da kyautata tsarin ba da kariyar tarihi da al’adu, don kare albarkatun al’adun kasar Sin.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa