HausaTv:
2025-11-03@08:55:53 GMT

Kasashen Gabashi Da Kudancin Afrika Zasuyi Taro Kan Rikicin Gabashin Kongo

Published: 4th, February 2025 GMT

Kasar Kenya mai rike da shugabancin kungiyar kasashen gabashin Afirka ta EAC, ta sanar cewa za’a gudanar da wani taron hadin gwiwa da kungiyar raya kasashen yankin kudancin Afirka ta SADC a ranar Juma’a a Dar es Salaam, babban birnin kasar Tanzania.

Taron na kwanani biyu zai samu halartar shugabannin kasashen Rwanda da Kongo, Paul Kagame da Félix Tshisekedi.

Al’amura sun dagule a yankin na gabshin Kongo bayan harin da ‘yan tawayen M23 – da Rwanda ke marawa baya suka kai a Goma, babban birnin Kivu ta Arewa, a makon jiya, da kuma fadan baya-bayan nan a Kudancin Kivu.

A cikin ‘yan kwanakin nan, kungiyoyin biyu da ke da ra’ayi daban-daban kan yadda za a warware rikicin, sun bayyana fatan shirya taron hadin gwiwa na gaggawa domin daidaita matsayarsu da kuma kaucewa hadarin da ke tattare da rikicin yankin. “

Manufar wannan babban taron it ace ci gaba da kokarin “sake tuntuba ta diflomasiyya don kawo karshen tarzomar” a gabashin DRC.

A wani labarin kuma Kwamitin Kare Hakkokin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya zai yi taro cikin gaggawa a ranar Juma’a domin duba rikicin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango da kuma tasirinsa kan ‘yancin bil’adama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 

Majalisar Shugabannin Kudancin Kaduna (SKLC) ta kammala shirye-shirye domin gudanar da gagarumar tarbar ga tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya).

Za a yi bikin ne domin tunawa da kyakkyawar rawar da majalisar ta ce ya taka a aikin soja da kuma hidimarsa ga kasa.

An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure

An shirya gudanar da bikin ne a ranar Asabar, 22 ga watan Nuwamba, 2025, a Babban Filin Wasan na garin Kafanchan, cibiyar kasuwancin Kudancin Kaduna.

A yayin taron majalisar karo na 19 da aka gudanar a Kafanchan, Shugaban SKLC, Ishaya Dare Akau, ya ce za a ba Janar Musa lambar yabo mafi girma ta majalisar wato GCSK.

Akau, ya ce wannan karramawar tana nuni da yadda Janar Musa ya wakilci Kudancin Kaduna, Jihar Kaduna, da Najeriya baki daya cikin kwarewa da cancanta, inda ya bayyana shi a matsayin jakada nagari.

A yayin taron, majalisar ta kuma kaddamar da kwamitin kula da harkokin kudi na Bikin Gargajiya na Shekara-shekara na Kudancin Kaduna (SKFEST), inda aka nada Shugaban Hukumar Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS), Comrade Jerry Adams, a matsayin shugaban kwamitin.

Manyan jami’an gwamnati da dama sun halarci taron karkashin jagorancin Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Henry Danjuma Magaji, tare da Mai ba Gwamna shawara kan harkokin siyasa, Hon. Ado Dogo Audu.

Sun yi wa majalisar bayani kan muhimman shirye-shiryen gwamnati, ciki har da amincewar da gwamnatin tarayya ta bayar na farfado da aikin gina hanyar Jere–Kagarko–Jaba–Kwoi–Kafanchan, wadda Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya taimaka wajen ganin tabbatuwarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa