Hamas Ta Ce An Fara Shawarwarin Tsagaita Wuta A Mataki Na Biyu
Published: 4th, February 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta sanar da fara shawarwarin tsagaita wuta a mataki na biyu tsakaninta da Isra’ila.
Kakakin Abdul Latif al-Qanou ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a kafar sadarwar zamani.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a tashar ta Telegram mai magana da yawun kungiyar Abdel Latif al-Qanoua ya zargi Isra’ila da “jinkirta aiwatar da ka’idojin jinƙai a yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma dakatar da aiwatar da hukuncin kisa.
Ya ce har yanzu kungiyar Falasdinu ta damu da batutuwa da dama da suka hada da matsuguni ga mutanen Gaza, da kuma kayan agaji da kuma kokarin sake gina yankin.
Al-Qanou ya kuma zargi Isra’ila da “katse” ka’idojin jin kai da ke kunshe cikin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da jinkirta” aiwatar da su.
Isra’ila ta ce ta aike da wata tawaga domin tattaunawa a mataki na gaba a tsagaita wuta mai rauni da kungiyar Hamas, wanda ke nuni da yiwuwar samun ci gaba gabanin ganawar firaminista Benjamin Netanyahu da shugaban Amurka Donald Trump a ranar Talata.
Bayanai sun ce Isra’ila ta ci gaba da keta yarjejeniyar ta hanyar kai hare-hare Gaza.
Isra’ila ta kama Falasdinawa akalla 380 tun bayan tsagaita bude wuta a Gaza inji kungiyoyi masu zaman kansu akasarinsu matasa a yankin Yammacin Gabar Kogin Jordan da aka mamaye tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
Tsohuwar jarumar Kannywood, Mansurah Isa, ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta yaɗa cewa wai tana son ta auri shahararren dan TikTok, Ashiru Mai Wushirya, wanda ya yi tashe a kafafen sada zumunta a ’yan kwanakin nan.
A wani saƙo da ta wallafa, Mansurah ta ce labarin ƙarya ne kuma ya jefa ta da iyalinta cikin ruɗani da damuwa.
Ta ce, “Na shiga firgici bayan na ga wannan labarin. Ba ni da wata alaka da Mai Wushirya. Wannan sharri ne tsagwaron karya.”
Rahoton da aka yada a jaridar AMC Hausa ya yi iƙirarin cewa wai Mansurah ta ce ta shirya auren Mai Wushirya idan har yana son ta da gaske.
Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin KebbiAmma jarumar ta yi watsi da wannan iƙirarin, tana mai cewa jaridar ta ɓata mata suna kuma ta karya ƙa’idojin aikin jarida.
Ta ce, “Na kira su, na ba su awa 24 su sauke labarin, amma har yanzu ba su yi hakan ba. Sun kira ni sun ba ni hakuri a waya, amma labarin har yanzu yana nan. Wannan abu ya zubar min da mutunci kuma ya saka iyalina cikin tashin hankali,” ina ji ta.
Mansurah ta bayyana cewa yanzu tana cikin shirin ‘WalkAwayCancer’, wani gagarumin shiri na wayar da kan jama’a kan mcutar daji, amma wannan labarin karya ya yi ƙoƙarin karkatar da hankalin mutane daga ainihin aikinta.
“Kun hana ni barci da kwanciyar hankali saboda labarin da babu gaskiya a cikinsa. Amma in sha Allahu, za ku ji daga gare mu,” in ji ta cikin fushi.
Har zuwa lokacin da muka kammala wannan labarin dai, kamfanin AMC Hausa bai fitar da wata sanarwa ba dangane da ƙarar da Mansurah ke shirin kai musu bisa zargin yaɗa labarin ƙarya.