Lebanon Ta Shigar Da Sabon Korafi Kan Isra’ila A Gaban Kwamitin Sulhu Na MDD
Published: 4th, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Labanon ta shigar da sabon korafi kan yahudawan sahyuniya gaban kwamitin sulhu na MDD, inda ta yi Allah wadai da hare-haren baya-bayan nan da yahudawan sahyuniya suka kai kan kasar Labanon, da kuma keta hurimun ikon kasar, da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma yau fiye da watanni biyu.
Wannan korafin, wanda aka mika ta hannun wakilcin Dindindin na Labanon a Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, ya jibanci yadda Isra’ila ta ci gaba da keta yarjejeniyar tun daga ranar 27 ga Nuwamba, 2024 ranar da tsagaita bude wuta ta fara aiki har zuwa yau Talata 4 ga Fabrairu.
Lebanon Ta yi Allah wadai da ci gaba da kai hare-hare ta kasa da ta sama da yahudawan sahyoniya suka yi, da barnata gidaje da matsugunan jama’a, da yin garkuwa da ‘yan kasar Lebanon da sojoji, da kuma hare-haren da ake kai wa fararen hula da ke kokarin komawa kauyukansu da ke kan iyakar kasar ta Lebanon.
Kusan ‘yan kasar Lebanon 24 ne suka yi shahada sannan wasu fiye da 124 suka jikkata a cikin wannan lokaci.
Kan ne kasar Lebanon ta yi kira ga kwamitin sulhu na MDD musamman kasashen da suka dauki nauyi da shiga tsakani wajen cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da su dauki kwararan matakai wajen tunkarar wadannan take-take, tare da yin matsin lamba kan Isra’ila ta mutunta dokokin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bayyana cewa: Babu wata tattaunawa da zata yi da Amurka a halin da take ciki na kare kanta
A yayin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan yankunan kasar Iran, a hukumance Iran ta bayyana rashin yiwuwar ci gaba da zaman tattaunawa da Amurka kan batun shirinta na makamshin nukuliya, tare da dora wa Amurka alhakin abin da ke faruwa kai tsaye.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Akwai hadin kai tsakanin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka wajen kai hare-hare kan kasar Iran domin rusa zaman tattaunawar nukiliya da haka ke bayyana kawar da duk wata magana ta hakikanin aniyar Amurka na samar da hanyar warware takaddamar Shirin Iran ta hanyar lumana.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa ci gaba da tattaunawa da Amurka a yayin da ake ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri yana gwada tsarin tattaunawar ba shi da ma’ana. Ya yi kakkausar suka ga matakin da hukumar ta IAEA ta dauka, inda ya yi la’akari da hakan a matsayin wani dalili na halasta cin zarafi a kan cibiyoyin nukiliyar Iran.