Masu zanga-zanga a birnin Kinshasa fadar mulkin kasar Dimokaradiyyar Kongo sun kai hare-hare kan ofisoshin jakadancin kasashe da suka hada da Amurka da Faransa

Masu zanga-zangar sun kai hare-hare a wasu ofisoshin jakadanci a birnin Kinshasa, fadar mulkin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, a lokacin da suke gudanar da zanga-zangar a makon da ya gabata, don nuna adawa da yadda ake ci gaba da ruruta wutar rikici a shiyar gabashin kasar.

Shafin sadarwa na yanar gizo na Russia Today ya bayyana cewa: Al’ummar Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango da suke cikin fushi sun kai hare-hare kan ofisoshin jakadancin kasashen Rwanda da Faransa da Belgium da kuma Amurka, yayin da hayaki ke tashi daga ginin ofishin jakadancin Faransa.

Masu zanga-zangar sun kona tutar Amurka tare da zargin kasashen yammacin duniya da goyon bayan ‘yan tawayen da suka karbe iko da birnin Goma da ke gabashin kasar.

A halin da ake ciki dai, sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban kasar Dimokaradiyyar Kwango Felix Tshisekedi, ya yi Allah wadai da harin da mayakan ‘yan tawayen M23 suka kai a birnin Goma.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce

Shugaba Samia Suluhu Hassan ta kasar Tanzania ta sake lashe zaɓen shugaban ƙasar mai cike da ruɗani.

Hukumomin zaɓen ƙasar sun sanar da cewa Shugaba Samia Suluhu ta lashe zaɓen ne da kashi 97 na kuri’un da aka jefa.

Hukamar zaɓen ƙasar ta bayyana cewa mutum 31,913,866 ne suka kaɗa kuri’a a zaɓen, wanda ya gudana a yayin da kasar ke fama da ƙazamar zanga-zanga.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa