Hukumar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta kasa NDLEA ta ce an yi wa wani mutum mai shekara 59 tiyata domin ciro sunƙin hodar ibilis 57 cikin guda 81 da ya haɗiye kwanaki bakwai da suka gabata a Addis Ababa da ke kasar Habasha.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi ya fitar, ta ce an kama mutumin ne a lokacin da ake tantance fasinjoji bayan isar su filin jirgin sama na Murtala Muhammad daga Habasha a ranar 26 ga watan da ya gabata.

Kakakin hukumar ya ce bincike ya gano cewa mutumin wanda ya yi iƙirarin ɗan kasuwa ne a yankin Oshodi da ke jihar Lagos, ya tafi Addis Ababa inda ya haɗiyi sunƙi 81 na hodar ibilis ɗin, daga bisani kuma ya hau jirgi zuwa Beirut da ke kasar Lebanon domin kaiwa a kan kuɗi dala 3000.

Ya kuma ce binciken nasu ya nuna cewa mutumin bai samu shiga ƙasar ba saboda kuɗin hannunsa ba su kai dala 2,000 ba da ake buƙata kafin shiga ƙasar ta Lebanon, wanda ya sa aka mayar da shi Addis Ababa inda ya yi yunƙirin fitar da miyagun ƙwayoyin amma ya kasa, daga nan kuma ya dawo Najeriya inda suka yi nasarar cafke shi.

Femi ya ƙara da cewa bayan kwanaki 5 ƙarƙashin sa idon hukumar a asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Lagos, mutumin ya yi kashin sunƙin hodar ibilis guda 24, inda daga bisani saboda gujewa kamuwa da rashin lafiya, aka yi masa tiyata domin cire sunƙi 57 da suka rage bayan uwargidansa da ɗan’uwansa sun amince da yin hakan.

bbc

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hodar Iblis

এছাড়াও পড়ুন:

Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran

Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai

Al’ummar Iran masu daraja!

Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.

Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.

A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.

Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.

Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita