Hukumar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta kasa NDLEA ta ce an yi wa wani mutum mai shekara 59 tiyata domin ciro sunƙin hodar ibilis 57 cikin guda 81 da ya haɗiye kwanaki bakwai da suka gabata a Addis Ababa da ke kasar Habasha.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi ya fitar, ta ce an kama mutumin ne a lokacin da ake tantance fasinjoji bayan isar su filin jirgin sama na Murtala Muhammad daga Habasha a ranar 26 ga watan da ya gabata.

Kakakin hukumar ya ce bincike ya gano cewa mutumin wanda ya yi iƙirarin ɗan kasuwa ne a yankin Oshodi da ke jihar Lagos, ya tafi Addis Ababa inda ya haɗiyi sunƙi 81 na hodar ibilis ɗin, daga bisani kuma ya hau jirgi zuwa Beirut da ke kasar Lebanon domin kaiwa a kan kuɗi dala 3000.

Ya kuma ce binciken nasu ya nuna cewa mutumin bai samu shiga ƙasar ba saboda kuɗin hannunsa ba su kai dala 2,000 ba da ake buƙata kafin shiga ƙasar ta Lebanon, wanda ya sa aka mayar da shi Addis Ababa inda ya yi yunƙirin fitar da miyagun ƙwayoyin amma ya kasa, daga nan kuma ya dawo Najeriya inda suka yi nasarar cafke shi.

Femi ya ƙara da cewa bayan kwanaki 5 ƙarƙashin sa idon hukumar a asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Lagos, mutumin ya yi kashin sunƙin hodar ibilis guda 24, inda daga bisani saboda gujewa kamuwa da rashin lafiya, aka yi masa tiyata domin cire sunƙi 57 da suka rage bayan uwargidansa da ɗan’uwansa sun amince da yin hakan.

bbc

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hodar Iblis

এছাড়াও পড়ুন:

Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi

Wani wanda ake zargi da safarar sassan jikin ɗan Adam ya shaida wa jami’an tsaro cewa ya shafe sama da shekara 10 yana sayar da sassan jikin mutum don samun kuɗi.

Dubun mutumin sun cika ne a ranar Asabar din da ta gabata inda sojoji suka kama shi a yankin Kulanla Odomoola da ke Jihar Ogun.

A furucinsa da ya amsa laifin, wanda ake zargin ya amince da sayar da sassan jikin mutum ga masu buƙata don samun kuɗin shiga.

“Na dogara ne da sayar da sassan jikin mutum tsawon shekaru 10 da suka gabata. Yawancin sassan da nake sayarwa ina tono su ne daga sabbin kaburbura a makabartu, yayin da wasu kuma nake samun su daga gawarwakin da aka watsar a gefen hanyoyi,” in ji shi.

Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

Wanda ake zargin, wanda ya amsa laifinsa ga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi kafin sojoji su cece shi, ana zargin yana kan hanyarsa ne na kai wani sassan jiki ga wani mai siye lokacin da aka kama shi.

Daga nan aka miƙa wanda ake zargin ga ’yan sanda a yankin Noforija don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

Laftanar Kanar Olabisi Olalekan Ayeni, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 81, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayan kama wanda ake zargin daga baya an miƙa shi tare da kayayyakin da aka samu a wurinsa, ga ’yan sandan Najeriya don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

“Sojojin sun ceto wanda ake zargin daga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115