Hamas Ta Yi Tir Da Shawarar Shugaban Amurka Ta Kwashe Falasdinawa Daga Gaza
Published: 2nd, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta yi Allah-wadai da kalaman shugaban Amurka Donald Trump kan mayar da mazauna Gaza zuwa kasashen Masar da Jordan dake makwabtaka da ita.
A cikin wata sanarwar da ya fitar, shugaban kungiyar Hamas Sami Abu Zuhri ya yi tir da irin wadannan shawarwari a matsayin “abin dariya kuma maras amfani,” yana mai cewa, “Abin da mamayar Isra’ila ta kasa cimma da karfi, ba zai samu ta hanyar makircin siyasa ba.
Abu Zuhri ya kara da cewa, “Sanarwar da Amurka ta nanata na raba Falasdinawa da gidajensu da nufin sake gina yankin zirin Gaza na nuni da yadda kasar ke da hannu wajen aikata laifukan da suka shafi yanki.”
Kana, ya yi gargadin cewa, “aikin kwashe mazauna Gaza” wani makirci ne na kara hargitsi da tashin hankali a yankin.
A ranar 25 ga watan Janairu ne dai Trump ya gabatar da wannan tsari mai cike da cece-kuce na kwashe Falasdinawa daga Gaza zuwa Masar da Jordan, wanda kasashen biyu suka ki amincewa da shi matuka.
Shi dai Shugaban Amurka Donald Trump ya jaddada kiransa ga kasashen Masar da Jordan domin su karbi Falasdinawan Gaza da suka rasa matsugunansu, duk da cewa kasashen Larabawan biyu sun yi watsi da shawararsa da ke cike da ce-ce-ku-ce.
Haka su ma kasashen Qatar, UAE da kuma Saudiyya sun yi fatali da shawarar da Trump ya bayar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bayyana cewa: Babu wata tattaunawa da zata yi da Amurka a halin da take ciki na kare kanta
A yayin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan yankunan kasar Iran, a hukumance Iran ta bayyana rashin yiwuwar ci gaba da zaman tattaunawa da Amurka kan batun shirinta na makamshin nukuliya, tare da dora wa Amurka alhakin abin da ke faruwa kai tsaye.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Akwai hadin kai tsakanin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka wajen kai hare-hare kan kasar Iran domin rusa zaman tattaunawar nukiliya da haka ke bayyana kawar da duk wata magana ta hakikanin aniyar Amurka na samar da hanyar warware takaddamar Shirin Iran ta hanyar lumana.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa ci gaba da tattaunawa da Amurka a yayin da ake ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri yana gwada tsarin tattaunawar ba shi da ma’ana. Ya yi kakkausar suka ga matakin da hukumar ta IAEA ta dauka, inda ya yi la’akari da hakan a matsayin wani dalili na halasta cin zarafi a kan cibiyoyin nukiliyar Iran.