SADC Zata Ci Gaba Da Wanzar Da Dakarunta A Gabacin Congo Duk Tare Da Nasarorin Da M23 Take Samu
Published: 2nd, February 2025 GMT
Shuwagabannin kungiyar kasashen raya tattalin arziki da kuma tsaron kasashen Afrika da kudu ta ce zasu ci gaba da wanzar da sojojinsu a kasar Congo duk tare da sauye-sauyen da kungiyar yan tawaye na M23 suka yi a yankin arewacin KIVU.
Shafin yanar gizo na Labarai ‘Africa News” ya bayyana cewa shuwagabannin kungiyar sun bada wannan sanarwan ne bayan wani taron gaggawa da suka gudanar a kasar Zibabwe a ranar Jumma’an da ta gabata.
Shugaban kungiyar na riko-riko kuma shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, ya yim kira ga kungiyar ta kasance mai nuna karfi da da kuma juriya kan abubuwanda da ke faruwa a arewacin congo.
Sojojin tabbatar da zaman lafiya na kungiyar a cikin makonnin da suka gabata sun fuskanci koma baya a hannun sojojin M23, inda suka kashe sojojin kungiyar kimani dozen guda daga kasashen na SADC.
Affirka ta kudu, Malawi, da Tanzania sun rasa sojoji a dai dai lokacinda sojojin M23 suka shiga birnin Goma babban birnin. A halin yanzu dai shugaba Tsetsekedi ya fara tattara sojojin kasar don kare birnin Kinshasa babban birnin kasar ta Congo.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir
Shugaban Majalisar Malamai na kungiyar Jama’atul Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS), Sheik Sani Yahaya Jingir, ya ce ba zai goyi bayan takarar Bola Tinubu ba a zaben 2027 matukar ya canza Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa.
Ya bayyana hakan ne yayin wani taron wa’azi a masallacinsa na ’Yan Taya da ke Jos, babban birnin jihar Filato.
Aminiya ta rawaito cewa a zaben 2023 da ya gabata dai Sheikh Jingir ya goyi bayan Tinubu sannan ya umarci magoya bayansa da su ma su yi haka a wancan lokacin.
Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — TrumpJita-jitar da ake yadawa dai a kan cewa akwai yiwuwar Tinubu ya ajiye Kashim din a matsayin abokin takararsa a zabe mai zuwa ta dada kamari a ’yan kwanakin nan.
To sai dai da yake nasa tsokacin a kan batun, malamin addinin ya ce, “Na ji akwai wasu mutane marasa kishin kasa daga ciki da wajen APC da ke kokarin lalata alakar da ke tsakanin Tinubu da Kashim domin cimma mummunar manufarsu. To mu ba ma maraba da wannan Shugaba Tinubu.
“Ni da wasu na kusa da ni mun goyi bayan Tinubu da Kashim, kuma za mu sake goyon bayan takararku a tare. Duk wani yunkuri sabanin haka ba na tare da shi kuma ba zan goyi baya ba saboda a baya sun amince su yi aiki tare.
“Na goyi bayansu ba tare da sun ba ni ko sisi ba. duk da yake ina da kusanci da Atiku, amma na ce Tinubu da Kashim zan yi. Akwai jita-jitar da ke yawo cewa dangantaka ta yi tsami a tsakaninsu, amma ni ban yarda da, na fi tunanin aikin makiya ne,” in ji malamin.
Sheikh Jingir ya kuma yi kira ga Shugba Tinubu da kada ya saurari masu kiran nasa da ya ajiye Kashim ya canza shi da wani a 2027, inda ya bayyana wadannan mutanen a matsayin marasa son ci gaba.