ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Kasashen Mali, Nijar Da Burkina Faso
Published: 2nd, February 2025 GMT
Kasashen 3 na yankin sahel sun kafa ta su kungiyar mai suna “Kawancen Sahel” (AES).
Yadda ficewar Nijar da Mali da Burkina Faso daga Ecowas ka iya raunata kungiyar Ficewar kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso daga kungiyar Ecowas a ranar Laraban nan bayan kwashen fiye da shekara guda ana zaman tankiya tsakanin kungiyar da kasashen guda uku, wani abu da ke nuni da rashin tabbas ga cigaba da kasancewar kungiyar ta Ecowas.
A ranar ta 29 ga watan Janairun 2024 ne kasashen guda uku da shugabannin mulkin soji ke jagoranta suka sanar da kungiyar Ecowas a hukumance dangane da bukatar ficewar tasu.
To sai dai bisa dokokin Ecowas, kasashen na bukatar sanar da kungiyar shekara guda kafin amincewa da ficewar.
Kuma a ranar Larabar nan ne wa’adin ke cika, bayan dukkan kasashen uku sun yi watsi da kiran kungiyar ta Ecowas na su kara tsawaita zamansu mambobinta na watanni shida domin samo mafita.
Yanzu dai kasashen na Burkina Faso da Mali da Nijar sun zama kawaye inda suka cure wuri guda karkashin kungiyar da suke kira Hadakar Kasashen Sahel (Allaiance of Sahel States (AES).
Shugabannin mulkin sojin kasashen dai sun zargi Ecowas da kakaba musu takunkumi na “rashin imani kuma haramtattu” bayan juyin mulkin da ya kawo su kan karaga.
Sun kuma yi amannar cewa kungiyar ta Afirka ta Yamma ba ta ba su cikakkiyar gudunmawa ba wajen yakar ‘yan’adda. Sun kuma yi amannar cewa Ecowas din ‘yar kanzagin tsohuwar uwar gijiyarsu ce wato Faransa.
Faransa ta kasance abokiyar hamayyar wannan kasashen da sojoji ke jagoranci da a yanzu haka suka kwammace yin hulda da kasashe irin su Rasha da Turkiyya da Iran.
‘ECOWAS ta raunana’
Kungiyar Ecowas dai ta samu rauni ne a watan Yulin 2023 bayan juyin mulkin jamhuriyar Nijar. Ecowas ta yi barazanar yin amfani da karfin soji wajen mayar da hambararren shugaban kasar, Bazoum Mohamed da kuma kakaba takunkuman tattalin arziki kan jamhuriyar wadanda yanzu duk an dage su.
Kasashen uku za su fito da nasu fasfo a ranar Larabar kuma sun sanar samar da rundunar sojin hadin gwiwa guda 5,000 da za su yaki masu ikrarin jihadi a yanki nan ba da jimawa ba.
Ficewar kasashen guda uku za ta yi wa Ecowas “illa musamman ta fuskarrikicin siyasa a yankin”, kamar yadda Gilles Yabi, shugaban kungiyar Wathi ta kwararru a Afirka ta Yamma, ya shaida wa AFP.
Hadakar kasashen guda uku na yankin Sahel, AES da wasu kasashen Ecowas na zaman tankiya. Misali Nijar ta ki amincewa ta bude iyakokinta ga jamhuriyar Benin wadda take zargi da bai wa ‘yanta’adda mafaka inda suke yin atisaye. Ta kuma zargi Nijeriya da kasancewa wani “filin daga na bayan gida” da ka iya yi mata illa.
Dukkanin kasashen biyu na Benin da Nijeriya sun musanta zarge-zargen makwabciyar tasu.
Togo da Ghana na zawarcin kungiyar AES
Kasar Togo ta kasance wadda ta bude tashar jirgin ruwanta ga kasashen uku na AES sannan kuma tana kokarin shiga tsakani.
“Togo tana da mafarki mai gajeren zango bisa hasashen da ake da su da suka shafi muradun tattalin arziki da zai illata Ecowas,” in ji Yabi.
Ministan harkokin wajen Togo a baya-bayan nan ya fadi cewa ba su cire ran cewa kasar tasa za ta shiga kungiyar ta AES ba.
Idan Ecowas ta rasa mamba ta hudu kamar Togo wadda ke da hanyoyin sufuri na ruwa, “za mu mamakin yadda Ecowas za ta rayu”, in Rinaldo Depagne, mataimakin darektan Afirka a kungiyar wanzar da zaman lafiya ta kasa da kasa ta ICG.
AES “na kakarin gamsar da kasashe cewa Ecowas ba ta yin komai sannan za su iya maye gurbinta,” in ji wata majiyar huldar jakadanci. “Sun fahimci cewa ba za su iya rayuwa su kadai ba.”
Ghana karkashin sabon shugaban kasarta, John mahama tana kokarin kai wa ga kasashen na AES. Dramani Mahama ya gana da shugabanninta sannan ya sanar cewa zai aike da jakadan na musamman zuwa kungiyar.
“Sabon shugaban kasar ya banbanta da mutumin da ya gada dangane da matsayar Ghana kan juyin mulkin da kasashen suka yi,” in ji Depagne na ICG.
“Tambayoyin da ake yi su ne ko za mu iya kasancewa a kungiyar AES da kuma Ecowas a lokaci guda?”
‘Sabuwar ECOWAS’
Abin da ya faru ya janyo muhawara kan bukatar kungiyar ta Ecowas “ta sake komawa ga muradunta na asali kan tattalin arziki da doka da dimokradiyya,” in ji Yabi.
“Kowa na sane da irin bukatar yin sauyi ga Ecowas domin cimma kungiyar Ecowas ta jama’a,” in ji wani minista na daya daga cikin kasashen Afirka ta yamma wanda ke tattaunawa da shugabannin mulkin sojin AES.
“AES ka iya zama tamkar dakin gwaji kuma za ta iya ci gaba da kasancewa mamba amma a sabuwar kungiyar Ecowas,” ya yi karin haske.
Duk da raunin da Ecowas din ta samu, Yabi ya ce dole ne mu karfafa dangantaka tsakanin kasashen AES da na Ecowas domin ” ci gaba da alakar tattalin arziki” sannan kuma mu fuskanci matsalar tsaro.
Masu ikrarin Jihadi sun haddasa mutuwar dubban jama’a a Mali da Nijar da Burkina Faso a tsawon shekaru 10 da suka gabata, sannan kuma rikicin ya fantsama zuwa kasashen kungiyar Ecowas kamar Benin da Togo.
কীওয়ার্ড: kungiyar Ecowas tattalin arziki kungiyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Yadda kasashen yammacin duniya suka ki sauke nauyin dake wuyansu, ya danne wa kasashe masu tasowa hakkinsu. Misali, a lokacin da ake samun bazuwar annobar COVID-19, dimbin kasashen yamma sun yi ajiyar alluran rigakafi a gida, inda suka hana fitar da su zuwa ketare, da musayar fasahohi masu nasaba da su. Sai dai a lokacin, hukumomi masu kula da harkokin kasa da kasa, kamar su Hukumar Lafiya ta Duniya, da Majalisar Dinkin Duniya dukkansu sun kasa tilasta musu sauya manufofinsu. Wannan tsarin kasa da kasa, idan mun bar shi haka ba tare da wani sauyi ba, to, wata rana za mu ga an koma tsarin zalunci na zamanin mulkin mallaka, wanda zai yi barazana ga hakkin rayuwa, da raya kai na al’ummar kasashe masu tasowa. Ta haka za mu san cewa gyara ya riga ya wajaba.
Saboda haka, shawarar inganta jagorancin duniya ta zama wani abun dake biyan bukatun dake akwai a duniyarmu. Wannan ya sa ta samun karbuwa a tsakanin kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka. Inda shahararren dan jarida a Najeriya Lawal Sale, ya rubuta a cikin wani sharhinsa cewa, “Wannan shawara za ta haifar da karin kwanciyar hankali, da tabbas a duniyarmu mai cike da tashin hankali, musamman ma a nahiyar Afirka.” Kana a nasa bangare, Paul Frimpong, wani shehun malami dan kasar Ghana, ya ce shawarar nan “tana tabbatar da cewa tsarin jagorancin duniya ba zai ci gaba da zama karkashin mallakar wasu kasashe masu karfi ba.” Kana dan jaridar kasar Lesotho, Silence Charumbira, ya ce shirin na baiwa kananan kasashe damar zama masu hakikanin ‘yancin kai.
Ta wannan shawara ta inganta jagorancin duniya, za mu iya kara fahimtar halayyar kasar ta Sin. Ko da yake wani yanayin da duniyarmu ke ciki shi ne dishewar tauraron kasashen yamma, amma duk da haka, kasar Sin ba ta neman yin koyi da kasashen yamma wajen yin babakere a duniya. Tana neman gyara, da inganta tsare-tsaren kula da harkokin duniya, ta yadda za ta tabbatar da moriyar dukkan kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa, maimakon kafa wani sabon tsari da ya saba wa tsarin kasa da kasa na yanzu. Dalilin da ya sa haka shi ne babban burin kasar Sin ta fuskar diflomasiyya, shi ne kafa al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga bil’adama, da kokarin tabbatar da ci gaban harkokinsu na bai daya.
Yayin da karin kasashe ke nuna goyon bayansu ga shawarar kula da al’amuran duniya da kasar Sin ta gabatar, tabbas za mu shaida hadin gwiwar karin mutane a duniya don neman wanzar da adalci, abin da zai haifar da damar tabbatar da daidaito da adalci a duniyarmu. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp