ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Kasashen Mali, Nijar Da Burkina Faso
Published: 2nd, February 2025 GMT
Kasashen 3 na yankin sahel sun kafa ta su kungiyar mai suna “Kawancen Sahel” (AES).
Yadda ficewar Nijar da Mali da Burkina Faso daga Ecowas ka iya raunata kungiyar Ficewar kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso daga kungiyar Ecowas a ranar Laraban nan bayan kwashen fiye da shekara guda ana zaman tankiya tsakanin kungiyar da kasashen guda uku, wani abu da ke nuni da rashin tabbas ga cigaba da kasancewar kungiyar ta Ecowas.
A ranar ta 29 ga watan Janairun 2024 ne kasashen guda uku da shugabannin mulkin soji ke jagoranta suka sanar da kungiyar Ecowas a hukumance dangane da bukatar ficewar tasu.
To sai dai bisa dokokin Ecowas, kasashen na bukatar sanar da kungiyar shekara guda kafin amincewa da ficewar.
Kuma a ranar Larabar nan ne wa’adin ke cika, bayan dukkan kasashen uku sun yi watsi da kiran kungiyar ta Ecowas na su kara tsawaita zamansu mambobinta na watanni shida domin samo mafita.
Yanzu dai kasashen na Burkina Faso da Mali da Nijar sun zama kawaye inda suka cure wuri guda karkashin kungiyar da suke kira Hadakar Kasashen Sahel (Allaiance of Sahel States (AES).
Shugabannin mulkin sojin kasashen dai sun zargi Ecowas da kakaba musu takunkumi na “rashin imani kuma haramtattu” bayan juyin mulkin da ya kawo su kan karaga.
Sun kuma yi amannar cewa kungiyar ta Afirka ta Yamma ba ta ba su cikakkiyar gudunmawa ba wajen yakar ‘yan’adda. Sun kuma yi amannar cewa Ecowas din ‘yar kanzagin tsohuwar uwar gijiyarsu ce wato Faransa.
Faransa ta kasance abokiyar hamayyar wannan kasashen da sojoji ke jagoranci da a yanzu haka suka kwammace yin hulda da kasashe irin su Rasha da Turkiyya da Iran.
‘ECOWAS ta raunana’
Kungiyar Ecowas dai ta samu rauni ne a watan Yulin 2023 bayan juyin mulkin jamhuriyar Nijar. Ecowas ta yi barazanar yin amfani da karfin soji wajen mayar da hambararren shugaban kasar, Bazoum Mohamed da kuma kakaba takunkuman tattalin arziki kan jamhuriyar wadanda yanzu duk an dage su.
Kasashen uku za su fito da nasu fasfo a ranar Larabar kuma sun sanar samar da rundunar sojin hadin gwiwa guda 5,000 da za su yaki masu ikrarin jihadi a yanki nan ba da jimawa ba.
Ficewar kasashen guda uku za ta yi wa Ecowas “illa musamman ta fuskarrikicin siyasa a yankin”, kamar yadda Gilles Yabi, shugaban kungiyar Wathi ta kwararru a Afirka ta Yamma, ya shaida wa AFP.
Hadakar kasashen guda uku na yankin Sahel, AES da wasu kasashen Ecowas na zaman tankiya. Misali Nijar ta ki amincewa ta bude iyakokinta ga jamhuriyar Benin wadda take zargi da bai wa ‘yanta’adda mafaka inda suke yin atisaye. Ta kuma zargi Nijeriya da kasancewa wani “filin daga na bayan gida” da ka iya yi mata illa.
Dukkanin kasashen biyu na Benin da Nijeriya sun musanta zarge-zargen makwabciyar tasu.
Togo da Ghana na zawarcin kungiyar AES
Kasar Togo ta kasance wadda ta bude tashar jirgin ruwanta ga kasashen uku na AES sannan kuma tana kokarin shiga tsakani.
“Togo tana da mafarki mai gajeren zango bisa hasashen da ake da su da suka shafi muradun tattalin arziki da zai illata Ecowas,” in ji Yabi.
Ministan harkokin wajen Togo a baya-bayan nan ya fadi cewa ba su cire ran cewa kasar tasa za ta shiga kungiyar ta AES ba.
Idan Ecowas ta rasa mamba ta hudu kamar Togo wadda ke da hanyoyin sufuri na ruwa, “za mu mamakin yadda Ecowas za ta rayu”, in Rinaldo Depagne, mataimakin darektan Afirka a kungiyar wanzar da zaman lafiya ta kasa da kasa ta ICG.
AES “na kakarin gamsar da kasashe cewa Ecowas ba ta yin komai sannan za su iya maye gurbinta,” in ji wata majiyar huldar jakadanci. “Sun fahimci cewa ba za su iya rayuwa su kadai ba.”
Ghana karkashin sabon shugaban kasarta, John mahama tana kokarin kai wa ga kasashen na AES. Dramani Mahama ya gana da shugabanninta sannan ya sanar cewa zai aike da jakadan na musamman zuwa kungiyar.
“Sabon shugaban kasar ya banbanta da mutumin da ya gada dangane da matsayar Ghana kan juyin mulkin da kasashen suka yi,” in ji Depagne na ICG.
“Tambayoyin da ake yi su ne ko za mu iya kasancewa a kungiyar AES da kuma Ecowas a lokaci guda?”
‘Sabuwar ECOWAS’
Abin da ya faru ya janyo muhawara kan bukatar kungiyar ta Ecowas “ta sake komawa ga muradunta na asali kan tattalin arziki da doka da dimokradiyya,” in ji Yabi.
“Kowa na sane da irin bukatar yin sauyi ga Ecowas domin cimma kungiyar Ecowas ta jama’a,” in ji wani minista na daya daga cikin kasashen Afirka ta yamma wanda ke tattaunawa da shugabannin mulkin sojin AES.
“AES ka iya zama tamkar dakin gwaji kuma za ta iya ci gaba da kasancewa mamba amma a sabuwar kungiyar Ecowas,” ya yi karin haske.
Duk da raunin da Ecowas din ta samu, Yabi ya ce dole ne mu karfafa dangantaka tsakanin kasashen AES da na Ecowas domin ” ci gaba da alakar tattalin arziki” sannan kuma mu fuskanci matsalar tsaro.
Masu ikrarin Jihadi sun haddasa mutuwar dubban jama’a a Mali da Nijar da Burkina Faso a tsawon shekaru 10 da suka gabata, sannan kuma rikicin ya fantsama zuwa kasashen kungiyar Ecowas kamar Benin da Togo.
কীওয়ার্ড: kungiyar Ecowas tattalin arziki kungiyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
Amurka ta sanar da kakaba takunkumi kan wasu kamfanoni 7 da ta ce suna da hannu wajen siyar da man kasar Iran, a wani mataki na kara matsin lamba duk da tattaunawar da aka yi kan shirin nukiliyar Iran.
Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar ta ce, bangarorion da takunkumin ya shafa sun hada da kamfanonin kasuwanci guda biyar, hudu da ke Hadaddiyar Daular Larabawa, daya kuma a kasar Turkiyya, wadanda suka sayar da albarkatun man fetur na kasar Iran ga kasashe uku, da kuma wasu kamfanonin jigilar kayayyaki guda biyu.
A cikin sanarwar da sakataren harkokin wajen kasar ta Amurka Marco Rubio ya fitar, ya ce “Matukar dai Iran na son samar da kudaden shiga na man fetur da sinadarai don samar da kudaden gudanar da ayyukanta na tabarbarewar zaman lafiya, da kungiyoyin da ya bayyana da na ta’addanci to Amurka za ta dauki matakin laftawa Iran da dukkan kawayenta alhakin kaucewa takunkumi.”
Matakin na zuwa ne jim kadan bayan Iran ta sanar da cewa za a sake gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa da gwamnatin shugaba Donald Trump a birnin Rome a ranar Asabar 3 ga watan Mayu a karkashin jagorancin kasra Oman.