Sojojin kasar Iran sun nuna karfinsu a yankin Asiya ta kudu tare da itisayen da ta yi ta gudanarwa a cikin yan makonnin da suka gabata. Tare da nuna iya diblomasiyyar kasar tare da sauran kasashen yankin.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Rear Admiral Habibollah Sayyari mataimakin shugaban rundunar sojiji na kasar yana fadar haka.

Ya kuma kara da cewa, iya diblomasiyyar kasar Iran a tsakanin  kasashen yankin, ya tabbatar da karfin da kasar take da shi a fagen karfin soje.

Kuma ta tabbatar da cewa zata iya kula da al-amuran tsarom da kuma tabbata shi a yankin. Sayyari yace an gudanar da atisayen na sojoji kimani rundunonin fiya da 100 inda suka yi musayar tunani da dabar barun yaki a tsakaninsu, inda da dama daga cikinsu sojojin kasashen waje ne.

Yace a cikin wadannan atisai daban-daban sun yi amfani da sabbin makamai da kasar ta kera da kuma sabbin dabarbarun yaki. Daga karshe Sayyari ya bayyana cewa mai suna ‘Zulfikar’ sojojin kasar Iran zasu nuna karfinsu a fagen kayakin aikin zamani da kuma sabbin dabarbarun yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Bor

Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe wani kwamandan ’yan ta’adda, Amir Abu Fatima da aka sanya ladar Naira miliyan 100 ga duk wanda ya kama shi ko ya tona asirin inda yake, aka kama shi.

Sojoji sun halaka Abu Fatima ne a wani samame na musamman da suka kai a yankin Arewacin Jihar Borno.

Majiyar leken asiri ta sanar da Zagazola Makama cewa an kai harin ne da sanyin safiyar Juma’a, a yankin Kukawa da ke yankin Tafkin Chadi.

Majiyoyin soji sun tabbatarwa da Zagazola Makama cewa, wannan aikin wani shiri ne da aka tsara a tsanake na halaka ‘yan ta’adda da nufin kashe Abu Fatima, wani babban jigo na ‘yan tada kayar baya.

Dakaru na musamman sun kutsa cikin yankin da ‘yan ta’addan suke  inda suka yi artabu da su a wani kazamin musayar wuta.

Abu Fatima ya samu munanan raunuka yayin arangamar kuma an kama shi da rai sai dai daga bisani ya mutu sakamakon zubar da jini da ya wuce kima sakamakon harbin bindiga da ya samu a yakin.

Majiyarmu ta bayyana cewa an kashe babban kwamandan sa na biyu, masu hada bama-bamai, da wasu mayaka da dama a samamen.

Kayayyakin da aka ƙwato daga farmakin sun hada da bindigogi kirar AK-47 da dama, da akwatunan harsasai  masu yawa, da kayan ƙera bama-bamai, da sauran kayan yaƙi.

Abu Fatima dai ya kasance cikin jerin sunayen da jami’an tsaro ke nema ruwa a jallo saboda hannu a hare-haren ta’addanci da dama a yankin Tafkin Chadi.

Ana kallon mutuwarsa a matsayin wani babban koma baya na aiki da tunani ga cibiyoyin ’yan ta’adda da ke aiki a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta hana tawagar kasashen Larabawa shiga gabar yammacin kogin Jordan
  • Aragchi: Shirin Nukliyar Kasar Iran Na Tafiya Kan Fahintar Rashin Amincewa Da Babakere
  • Iran Ta Kaddamarda Sabbin Magunguna Har 23 Tare Riga Kafin HPV A Karon Farko A Kasar
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  • Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
  • Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Bor
  •  DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       
  • Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku