Bisa alkaluman da hukumar kula da zirga-zirgar layin dogo ta kasar Sin ta bayar, tun daga kaddamar da zirga-zirgar fasinjoji a lokacin bikin bazara na Sin daga ranar 14 zuwa ranar 30 ga watan Janairu, yawan fasinjojin da jiragen kasa suka dauka ya kai miliyan 206 a kasar, kuma an yi zirga-zirgar fasinjojin cikin kwanciyar hankali.

Yayin bikin, hukumomin kula da layin dogo na sassan kasar sun kara karfin aiki a wuraren da aka fi amfani da su, da inganta karfin ba da hidimmomin jiragen kasa da tashoshi, da aiwatar da matakan saukakawa jama’a, da kuma kokarin samar wa fasinjoji ingantacciyar hanyar tafiya.

Alal misali, reshen Beijing na kamfanin kula da layin dogo na kasar Sin, ya kara tashoshin caji a tashar jiragen kasa ta yammacin Beijing don biyan bukatun fasinjoji na cajin na’urorin lantarki. Shi kuwa reshen Chengdu na kamfanin layin dogo na kasar Sin, ya kafa tashoshin kulawa da kofofin shiga da wuraren binciken tsaro dake cikin manyan tashoshin jiragen kasa a birane 53, ciki har da tashar gabashin Chengdu da tashar arewacin Chongqing, don ba da fifiko ga fasinjoji na gaggawa da fasinjoji masu rauni kamar tsofaffi, yara, marasa lafiya, nakasassu da mata masu juna biyu cikin mintuna 15 kafin jirgi ya tashi. A Urumqi kuwa, kamfanin layin dogo na kasar Sin ya sanya akwatunan ba da hidimomi a jiragen kasa, wadanda suke samar da abubuwa kamar kayayyakin hana sauraron sauti ta kunne da marufin ido da ba za a iya sake amfani da su ba.(Safiyah Ma)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: layin dogo na jiragen kasa

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta zargi Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da kin yin adalci wurin ayyuka da raba mukamai tsakanin Arewa da Kudancin Kasar nan.

Wadannan zarge-zarge suka sa fadar Shugaban Kasa ta hannun mai taimaka masa na musamman kan kafofin yada labarai Bayo Onanuga mayar da martani ga kungiyar ta ACF.

Ko wadanne irin martani fadar shugaban kasar ta mayar ga kungiyar?

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  •  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha
  • MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar