Nijeriya Na Da Dimbin Dukiyar Da Tinubu Zai Rika Tafiye-tafiye Zuwa Kasashen Waje – Minista
Published: 31st, January 2025 GMT
Da yake magana ta cikin shirin siyasa na talabijin Channels, ministan ya ce, shugaban kasa bai yi wasu tafiye-tafiyen da suka isa ba.
“Har yanzu wannan gwamnatin sabuwa ce. An rantsar da shi a 2023. Ta fuskancin duniya har yanzu shi sabon shugaban kasa ne. Yana bukatar tattaunawa da ganawa da takwarorinsa domin gina alaka mai kyau a tsakaninsu, sannan kuna iya ganin amfanun irin wadannan tafiye-tafiyen.
“Za ka sake tafiya ka samu zuba jari na dala biliyan 2 kamar yadda ya yi a Brazil. A zahiri, ba mu ma yi tafiye-tafiyen da suka isa ba. Ina ba da shawarar mu sake yin wasu karin tafiye-tafiyen.
“Nijeriya tana da dinbin dukiya. Nawa ne tafiyar zai lakume idan aka kwatanta da amfanin da hakan zai samar. Sannan, yanzu nawa ne ma kudin idan ka kwatanta da abubuwan da shugaban kasa ya riga ya shawo kansu.
“Nawa muke barnatarwa a tallafin mai, wutar lantarki da sauran tallafi,” ministan ya tambaya.
এছাড়াও পড়ুন:
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
Da yake mayar da martani ga wannan zargin na Amurka, Bwala ya ce gwamnatin Tinubu tana jajircewa wajen kare dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da addini ba, yana mai cewa Amurka da Nijeriya sun dade suna hadin gwiwa a yaki da ta’addanci.
“Shugaba Bola Tinubu da Shugaba Donald Trump suna da kudiri iri ɗaya a yaƙi da ta’addanci da duk wani nau’in ta’addanci a kan bil’adama,” in ji Bwala.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA