Fannonin Da Xi Jinping Ya Lura Da Su A Ziyararsa A Arewa Maso Gabashin Sin
Published: 29th, January 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kan yi rangadi a wurare daban daban kafin bikin bazara na kasar, kana kafin bikin na wannan shekara, shugaban ya ziyarci lardin Liaoning dake arewa maso gabashin Sin. Sai dai wadanne fannonin ya mai da hankali a kai, yayin wannan ziyara?
Abu na farko da shugaba Xi ya lura da shi, shi ne aikin sabunta fasahohin masana’antu.
Sa’an nan abu na biyu da shugaba Xi Jinping ya sa lura a kai shi ne yadda ake kula da jama’ar da bala’in ambaliyar ruwa ya ritsa da su a bara. Yayin da fanni na uku shi ne yadda kasuwannin wurin suke samar da isasshen kayayyakin abinci masu inganci ga jama’a, a lokacin bikin bazara na gargajiya.
Cikin wata unguwa, shugaba Xi ya ce, wani abu mafi faranta rai shi ne ganin yadda jama’a suke jin dadin rayuwa. Ya ce ya kamata a kara kokarin tabbatar da haka a ko da yaushe. (Bello Wang)
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.
A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.
Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.