Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa Ta Ce: Dokokin Da Isra’ila Ta Gindaya Mata Bala’i Ne
Published: 29th, January 2025 GMT
Babban kwamishinan hukumar kula da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya “UNRWA” ya bayyana wa kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya cewa: Aiwatar da dokokin Isra’ila kan hukumar UNRWA zai zama bala’i
Babban Kwamishinan Hukumar Kula da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya (UNRWA), Philippe Lazzarini, ya ce: Aiwatar da cikakken dokar Majalisar Dokokin Haramtacciyar kasar Isra’ila ta Knesset kan hukumar UNRWA zai zama masifa, yana mai gargadin cewa: Rage ayyukan hukumar ta “UNRWA” a wajen tsarin siyasa, kuma a daidai lokacin da kwarin gwiwa daga kasashen duniya ya yi kadan, wanda hakan zai kawo cikas ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.
Shafin watsa labaran Falasdinu na “Wafa” ya bayar da rahoton cewa: A jawabin da ya gabatar ga zaman kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya kan halin da ake ciki a yankin gabas ta tsakiya, gami da batun Falasdinu, a halin yanzu, Lazzarini ya jaddada cewa: Hukumarsa tana da matukar muhimmanci wajen tallafa wa al’ummar da suka shiga halin kaka-ni ka yi da kuma ci gaba da wanzar da yarjejeniyar dakatar da bude wuta, amma duk da haka a cikin kwanaki biyu, ayyukan hukumar ya tsaya cak a yankunan Falasdinawa.
Ya yi gargadin cewa: Makomar miliyoyin Falasdinawa, da tsagaita bude wuta da kuma fatan samun mafita ta siyasa da za ta samar da dawwamammen zaman lafiya da tsaro na cikin hadari.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u
A yau Asabar ne kasar Sin ta yi nasarar harba tauraron dan Adam na lura da yanayin bala’u a doron kasa, wanda ake sa ran zai rika samar da bayanai ga kasar Sin dangane da aukuwar bala’u daga indallahi, ta aikewa da sakwanni tsakanin sararin samaniya zuwa doron duniya.
An harba tauraron dan Adam din mai suna Zhangheng 1-02, ta amfani da rokar Long March-2D, daga tashar harba kumbuna ta Jiuquan dake arewa maso yammacin kasar Sin, da karfe 4 saura mintuna 4 agogon Beijing, ya kuma shiga da’irarsa ba tare da wata matsala ba, kamar dai yadda hukumar kula da binciken sararin samaniya ta kasar Sin ko CNSA ta tabbatar.
Kazalika, CNSA ta ce, wannan aiki muhimmin mataki ne da Sin ta taka, a turbar nazarin yanayin doron kasa na zahiri. An sanyawa tauraron sunan wani shahararren mai kirkire-kirkire na kasar Sin, wato marigayi Zhang Heng, wanda shi ne mutum na farko a duniya, da ya kago na’urar “seismoscope” ta hasashen aukuwar girgizar kasa, shekaru sama da 1,800 da suka gabata, kuma an samar da tauraron ne da hadin gwiwar Sin da kasar Italiya. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp