Leadership News Hausa:
2025-05-01@00:39:43 GMT

Tinubu Ya Yi Alƙawarin Inganta Wutar Lantarki A Nijeriya

Published: 29th, January 2025 GMT

Tinubu Ya Yi Alƙawarin Inganta Wutar Lantarki A Nijeriya

Tinubu ya gode wa shugaban Bankin Duniya, Ajay Banga, da shugaban Bankin Raya Ƙasashen Afirka, Akinwumi Adeshina, saboda ƙoƙarinsu na samar da karin wutar lantarki a Afirka.

Ya kuma ce yadda masu zuba jari ke gamsuwa da shirye-shiryen gwamnatinsa ya sa aka samu jarin dala biliyan shida a ɓangaren samar da makamashi a shekarar da ta gabata.

Hukumar IFC ta sanar da cewa za ta saka dala miliyan 70 domin taimaka wa ‘yan kasuwa su samar da wutar lantarki ta hanyoyin da ba sa gurɓata muhalli.

Rahotanni sun nuna cewa Nijeriya na buƙatar aƙalla dala biliyan 23.2 domin inganta ɓangaren wutar lantarki da tabbatar da wadatarta ga al’umma.

Taron ya samu halartar shugabannin ƙasashen Afirka da dama, ciki har da shugabannin Afirka ta Kudu, Ghana, Rwanda, Tanzania, da kuma mataimakiyar Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed.

Sauran mahalarta sun haɗa da shugaban Bankin Duniya, Ajay Banga, da shugaban Bankin Raya Ƙasashen Afirka, Akinwumi Adeshina, da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Alƙawari Wutar Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu

Tsoffin ma’aikatan Hukumar Shirya Jarabawar (NECO), da suka yi ritaya na neman a biya su haƙƙoƙinsu da suke bin bashi.

Shugaban ƙungiyar tsofffin ma’aikatan, Dokta Abdullahi Rotimi Williams ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar da hedikwatar kungiyar a Minna, babban birnin Neja.

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya

Shugaban ya kuma koka kan yadda gwamnatin Nijeriya ta maida ritaya abin fargaba a wurin ma’aikata saboda tarin ƙalubalen da ke biyo bayan hakan, musamman maƙalewar haƙƙoƙinsu.

“Da yawa tsoron ritaya ake yi yanzu. Don haka wannan ƙungiyar za ta taimaka wajen rage waɗannan matsalolin.

“Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne na lafiya. Don haka ina roƙon shugaban hukumar da ya tabbatar cewa daga yanzu an kammala shirye-shiryen da suka kamata kafin ma’aikacin NECO ya yi ritaya.”

Ya kuma ce duk da jagororin hukumar na yanzu sun biya wasu daga cikin haƙƙoƙin nasu, ba a kai ga biyan alawus ɗin ƙarin girma ba, da na tafiye-tafiye ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine