Hadakar Kasashen Sahel Sun Yi Ban Kwana Da Kungiyar ECOWAS
Published: 29th, January 2025 GMT
Hadakar Kasashen Sahel na AES, sun yi ban kwana da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS ko CEDEAO a hukumance bayan shekaru 50 na kasancewa mamba a cikinta.
Ya zuwa wannan Laraba, 29 ga Janairu, bangarorin biyu sun raba gari duk da cwa kungiyar ta ECOWAS ta baiwa kasashen wa’adin watannin shida ko zasu canza ra’ayi.
Kasashen na Mali, Nijar da kuma Burkina Faso sun ce bakin alkalami ya riga fa ya bushe.
A jiya Talata al’umomin kasashen guda uku sun gudanar da gangami da jerin gwano na nuna murnar ficewa daga kungiyar da suka ce ta zama ‘yar amshin shatan kasashen yamma musamman faransa wacce ta yi musu mulkin mallaka.
Haka zalika a wannan Larabar ce kasashen uku zasu kaddamar da fasfonsu, amma sun ce masu rike da fasfon Ecowas zasu ci gaba da amfani da shi, kuma sauren al’umomin kasashen ECOWAS zasu ci gaba da shige da fice cikin ‘yanci.
Matakin Kasashen na AES bai shafi kungiyar UEMOA ta kasashe guda 8 da ke anfani da kudin bai daya na sefa ba, Don haka ‘yancin zirga-zirgar jama’a da kayayyaki ya kasance tabbatacce a wannan yanki wanda ya hada kasashen Ivory Coast, Senegal da Benin.
A ranar 28 ga watan Janairu 2024, kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar suka ba da sanarwar ficewa daga kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka. Hakan ya biyo bayan kirkirar kungiyar AES na Kawancen Sahel a ranar 6 ga watan Yulin 2024.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Jamhuriyar Nijar.
Mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad-Reza Aref ya ce Iran na ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar da sauran kasashen nahiyar Afirka bisa tsarin juyin juya halin Musulunci.
Aref ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da ministan man fetur na kasar Nijar Sahabi Oumarou wanda ke Tehran, inda yake jagorantar wata tawaga, domin halartar taron hadin gwiwar tattalin arzikin Iran da Afirka karo na uku.
Ya ce da gaske ne gwamnatin Iran mai ci a yanzu tana son raya dangantakar da ke tsakaninta da kasashen Afirka ciki har da Nijar dangane da batutuwan da suka dace.
Ya kara da cewa, “Kasancewar manyan jami’an Nijar a taron da kuma kwamitin hadin gwiwa wani mataki ne mai ban sha’awa na inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.”
Mataimakin shugaban kasar ya jaddada cewa, bunkasa alaka da Nijar abu ne mai matukar muhimmanci, “idan aka yi la’akari da matsayinta kan ci gaban yanki da na kasa da kasa da kuma ra’ayi daya kan batutuwan Falasdinu da Lebanon.”
A yayin da yake tsokaci ga kiran da ministan na Nijar ya yi na inganta alaka a fannin noma, man fetur, da makamashi mai dorewa, Aref ya bayyana wadannan fannoni guda uku a matsayin muhimman batutuwan da suka shafi dangantakar Iran da Nijar, wadanda ya ce kwamitin hadin gwiwa zai duba su.
Yayin da yake tsokaci kan dangantakar tattalin arziki, ya ce, ya kamata kamfanoni masu zaman kansu na kasashen biyu su zuba jari don ciyar da matakin hadin gwiwa zuwa matsayi mafi girma.