Shugaban Amurka Ya Gabatar Da Shirin Tilastawa Falasdinawa Mazauna Gaza Yin Gudun Hijira
Published: 28th, January 2025 GMT
Kalaman shugaban Amurka na cewa zai tsarkake Zirin Gaza na Falasdinu ta ruda kawayen kasarsa na Larabawa tare da hargitsa su
Wani mai sharhi na jaridar Washington Post David Ignatius ya ce kalaman shugaban Amurka Donald Trump na tsarkake Gaza da mika Falasdinawa zuwa Masar da Jordan ya sanya kasashen Larabawa da suke kawancen da Amurka cikin halin fargaba da dardar.
Shafin watsa labaran Al-Quds Al-Arabi, ta yi nuni da cewa Trump ya gabatar da tunaninsa domin hanyar gabatar da shawarwari da tunani tana da dama tare da sabani da siyasa a aikace. Ta ce Trump na fuskantar daukan matakin yin kasadar da zai lalata kyawawan ra’ayinsa da bayyana munanan tunaninsa. Jaridar ta kara da cewa: shugaban na Amurka zai tafka babban kuskure a manufofin siyasar na harkokin waje tun farko fara gudanar da mulkinsa karo na biyu, a lokacin da ya firgita manema labarai inda ya shaida musu cewa yana so ya share ‘yan Gaza daga mazaunansu tare da kwashe wasu daga cikinsu zuwa kasashen Jordan da Masar.
Akwai yiwuwar shawarar Trump ta zo ne a matsayin ra’ayinsa na kashin kansa, ba hakikanin siyasar da zai aiwatar a zahiri ba, sai dai fitar kalaman a fili ta bai wa shugabannin Larabawa masu sassaucin ra’ayi da suke neman yin aiki da shi ta wurga su cikin mamaki, domin canjawa Falasdinawa wurin zama lamari ne da zai dagulawa gwamnatocin kasashen Larabawa masu sassaucin ra’ayi lissafi a duk yankin.
Ignatius ya kara da cewa: Trump a matsayinsa mai son kawo rudani zai iya furta kalaman a matsayin ra’ayinsa na tabbas a fagen siyasarsa a yankin Gabas ta Tsakiya, wadda ta kasance kamar jefa bama-bamai kan kasashen Larabawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
Fadar Shugaban ƙasa ta bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarin wa’adin shekara guda ga shugaban hukumar Kwastan ta Nijeriya, Bashir Adewale Adeniyi.
Kafin wannan ƙarin wa’adin, aikin Adeniyi zai kare ne a ranar 31 ga Agusta, 2025. Sai dai sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis ta ce wannan mataki na Tinubu zai ba Adeniyi damar kammala muhimman gyare-gyare da ayyuka da gwamnatin ke aiwatarwa a hukumar.
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da GidajeA cikin manyan ayyukan da ake son a kammala akwai shigar da cigaban zamani da ake yi wa hukumar Kwastan, da aiwatar da tsarin “National Single Window Project” da kuma cika alƙawuran Nijeriya a ƙarƙashin yarjejeniyar cinikayyar Afrika (AfCFTA).
“Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya” in ji sanarwar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp