Shugaban Amurka Ya Gabatar Da Shirin Tilastawa Falasdinawa Mazauna Gaza Yin Gudun Hijira
Published: 28th, January 2025 GMT
Kalaman shugaban Amurka na cewa zai tsarkake Zirin Gaza na Falasdinu ta ruda kawayen kasarsa na Larabawa tare da hargitsa su
Wani mai sharhi na jaridar Washington Post David Ignatius ya ce kalaman shugaban Amurka Donald Trump na tsarkake Gaza da mika Falasdinawa zuwa Masar da Jordan ya sanya kasashen Larabawa da suke kawancen da Amurka cikin halin fargaba da dardar.
Shafin watsa labaran Al-Quds Al-Arabi, ta yi nuni da cewa Trump ya gabatar da tunaninsa domin hanyar gabatar da shawarwari da tunani tana da dama tare da sabani da siyasa a aikace. Ta ce Trump na fuskantar daukan matakin yin kasadar da zai lalata kyawawan ra’ayinsa da bayyana munanan tunaninsa. Jaridar ta kara da cewa: shugaban na Amurka zai tafka babban kuskure a manufofin siyasar na harkokin waje tun farko fara gudanar da mulkinsa karo na biyu, a lokacin da ya firgita manema labarai inda ya shaida musu cewa yana so ya share ‘yan Gaza daga mazaunansu tare da kwashe wasu daga cikinsu zuwa kasashen Jordan da Masar.
Akwai yiwuwar shawarar Trump ta zo ne a matsayin ra’ayinsa na kashin kansa, ba hakikanin siyasar da zai aiwatar a zahiri ba, sai dai fitar kalaman a fili ta bai wa shugabannin Larabawa masu sassaucin ra’ayi da suke neman yin aiki da shi ta wurga su cikin mamaki, domin canjawa Falasdinawa wurin zama lamari ne da zai dagulawa gwamnatocin kasashen Larabawa masu sassaucin ra’ayi lissafi a duk yankin.
Ignatius ya kara da cewa: Trump a matsayinsa mai son kawo rudani zai iya furta kalaman a matsayin ra’ayinsa na tabbas a fagen siyasarsa a yankin Gabas ta Tsakiya, wadda ta kasance kamar jefa bama-bamai kan kasashen Larabawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya zargi Isra’ila da yin zagon kasa ga diflomasiyya ta hanyar tsallaka jajayen layukan kasar Iran, da kuma ta’azzara rikici da kasashen yammacin duniya, yana mai bayyana cewa, ba za a iya yin shawarwari a halin da ake ciki ba.
Sanarwar dai na nuni da koma baya sosai a yunkurin diflomasiyya na Iran da kasashen Yamma, musamman yadda tashe-tashen hankula ke kara ta’azzara bayan matakin sojin Isra’ila.
Matakin na Isra’ila da hadin kai tare da Amurka na a matsayin kokari na kawar da duk wata dama ta cimma sakamakon shawarwari.
“Ba za a iya shawarwarin ba yayin da a lokaci guda ake barin gwamnatin kisan kare dangi ta kai hari kan Iran.”
“Ba Isra’ila za ta aikata irin wadannan laifuka ba tare da amincewar Amurka ba.”
Iran dai na kallon hare-haren da Isra’ila ta kai a baya-bayan nan a matsayin wani hari kai tsaye ga ‘yan kasarta.