Leadership News Hausa:
2025-09-18@04:14:37 GMT

A Banza Man Kare: Barazana Da Takunkumi Sun Daina Tasiri

Published: 28th, January 2025 GMT

A Banza Man Kare: Barazana Da Takunkumi Sun Daina Tasiri

Yanzu shekarar ta 2025 muke ciki, kuma matakin da duniya ke daukawa wajen gudanar da al’amura ya bambanta da shekaru goma da suka gabata. Amma abin takaici shi ne, wasu har yanzu sun nace ma tsoffin dabaru, suna ganin barazanar haraji da takunkumi na iya mamaye duniya, na san kun riga kun san inda na dosa.

Shugaban Amurka Donald Trump da aka rantsar a baya-bayan nan ya yi barazanar sanya harajin kashi 100 bisa 100 kan kasashen BRICS idan suka ci gaba da kokarin rage tasirin dala. “A matsayinsu na al’ummar BRICS, za a kakaba musu harajin kashi 100 bisa 100 idan har suna tunanin aiwatar da abin da suke tunani, don haka za su yi watsi da hakan nan take.” Wannan na daga cikin kalamansa a ranar farko da ya hau kan karagar mulki. Muna iya cewa wannan na daya daga cikin sumbatunsa da ya saba yi, saboda sanin kowa ne cewa, ba a kafa BRICS don ta yi jayayya, ko sa-in-sa da kowa ba, sai dai don karfafa hadin gwiwa da samun wadata, kuma gaskiyar magana ita ce, yanzu kasashen duniya sun daina tsoron mamayar kudin wata kasa ko matsin lamba na takunkumi.

Mu dauki Rasha a matayin misali, lokacin da ta fuskanci dimbin takunkumi daga kasashen yamma a 2014 da 2022, da yawa sun yi hasashen durkushewar tattalin arzikinta. Maimakon haka, Rasha ta samar wa kanta mafita ta hanyar tsarin hada-hadar kudi na cikin gida wato SPFS, wanda ba ya bukatar tsarin hada-hadar kudi na yammacin duniya, wannan yunkurin ya yi wa tattalin arzikin Rasha garkuwa tare da aza harsashi na zurfafa dangantakar hada-hadar kudi da kawayenta kamar Turkiya, Kazakhstan, har ma da al’ummomi a Gabas ta Tsakiya, tare da yin watsi da tsarin kasashen Yamma. Hakazalika, Amurka ta hana Turkiya damar amfani da fasaha da wasu kayayyakin aiki na Amurka, kama daga jiragen F-35 zuwa jiragen sama marasa matuka. Sakamakon haka shi ne, a halin yanzu Turkiya na kera wasu daga cikin wadannan kayayyakin aiki da albarkatunta har ma ta fara fitar da kayayyaki zuwa wasu kasashen Gabas ta Tsakiya da Afirka. Haka ma kasashen BRICS su ma sun yi ta sake fasalin ka’idojin cinikayyar duniya. Sun koma ga amfani da nasu kudade wajen gudanar da kasuwanci a tsakaninsu, suna rage dogaro da dalar Amurka. Hakazalika, Brazil da Sin na yin cinikayya da kudaden kasashensu, matakin da Indiya da kawayenta na yankin suke koyi da su. Yanzu dai kan mage ya waye, kuma kasashen duniya sun fahimci cewa hadin gwiwar samun moriyar juna tare da dunkulewar duniya waje guda su ne mafita ga kalubalen da duniya ke fuskanta, kuma wannan shi ne makasudin kafa BRICS. (Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar

Jami’an kasashen larabawa da na Musulmi sun bukaci daukar kwararan matakai kan Isra’ila bayan harin da ta kai a birnin Doha, inda suka bayyana harin a matsayin “na matsorata, da muggan laifuka.”

Da yake jawabi a gun taron ministocin harkokin wajen kasashen a birnin Doha, Sakatare-Janar na kungiyar kasashen Larabawa Ahmed Aboul Gheit ya ce harin, ha’inci ne da wauta.”

Sakatare-Janar na Kungiyar ya bayyana “cikakken goyon baya” ga Qatar bayan abin da ya kira “cin zarafin Isra’ila”, yana mai jaddada cewa dole ne kasashen duniya su dauki kwakkwaran mataki kan Tel Aviv.

Shi ma da yake jawabi a taron share fagen kasashen musulmin da na Larabawa, firaministan Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani ya yi tir da harin da ya danganta da na “ta’addancin kasa” da kuma keta duk wani yunkuri na shiga tsakani.”

Sheikh Abdulrahman Al Thani ya bukaci kasashen duniya da su daina yin Magana mai tamkar harshen damo, su kuma hukunta Isra’ila saboda “laifin” da ta aikata.

Ya yi wannan jawabi ne a wani taron share fage da aka yi a jajibirin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Musulunci da Qatar ta shirya bayan da Isra’ila ta kai wani hari irinsa na farko kan kasar a kan shugabannin Hamas a Doha. Yau Litinin ne shugabannin kasashen na Larabawa da na Musulmi zasu hadu a birnin Doha domin tattauna batun.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa