Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa Nijeriya na da wadataccen arzikin da za ta ci gaba da ɗawainiyar duk wasu tafiye-tafiyen Shugaba Bola Tinubu zuwa ƙetare.

A bayan nan dai ’yan Nijeriya na ci gaba da bayyana damuwa kan yawan tafiye-tafiyen da shugaban ƙasar ke yi a kai-a kai zuwa ƙetare la’akari da tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.

Da kuɗin hayar gidana da ke Kaduna nake sayen abinci a yanzu — Buhari ’Yan sanda sun yi ƙarin haske kan barazanar harin ’yan ta’adda a Kano

Ana kuma ci gaba da jefa ayar tambaya ko shin tafiye-tafiyen da shugaban ƙasar ke yi suna haifar da ɗa mai ido ta hanyar kalato wa ƙasar wata riba.

Sai dai a yayin da ya bayyana a Shirin Politics Today na Gidan Talabijin na Channels, Ministan ya kare matakin tafiye-tafiyen da shugaban ke yi a kai a kai.

Ya bayyana cewa, duk da ƙorafe-ƙorafen da ake yi, a halin yanzu ma akwai buƙatar shugaban ƙasar ya ƙara yawan tafiye-tafiyen saboda muhimmancin hakan wajen janyo wa ƙasar alfanu.

Ministan ya ce ta hanyar inganta alaƙar Nijeriya da sauran shugabannin ƙasashen duniya ne Shugaba Tinubu zai ɗora ƙasar kan turbar zuwa tudun tsira.

“Irin wannan ƙididdigar ƙwazo da ake yi wa gwamnatin a halin yanzu ba daidai ba ne domin kuwa har yanzu sabon shugaba ne a Nijeriya la’akari da cewa a shekarar 2023 ya shiga ofis.

“Saboda haka yana buƙatar ya mu’amalanci takwarorinsa shugabannin ƙasashen domin ƙulla dangantaka da su.

“Ko a bayan nan mun ga yadda aka ci ribar hakan [tafiye-tafiyen] da ta janyo wa ƙasar nan zuba jari na kimanin dala biliyan 2 daga ƙasar Brazil. Saboda haka abin da zan ce a yanzu akwai buƙatar a ƙara yawan tafiye-tafiyen.

Tuggar ya musanta zargin cewa Nijeriya ba ta da wadataccen arzikin da a riƙa ɗawainiyar waɗannan tafiye-tafiyen.

“In dai dangane da wannan mas’ala ce Nijeriya tana da arziki. Duka nawa ake kashewa wajen tafiye-tafiyen idan an kwatanta da ribar da ake samu a hakan?

“Sannan duka nawa ake kashewa idan an kwatanta da waɗansu ayyuka da shugaban ƙasar ya aiwatar a dalilin hakan?

Tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, Tinubu ya ziyarci aƙalla ƙasashen duniya 19 a tafiye-tafiye 32 da ya yi zuwa ƙetare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yusuf Tuggar shugaban ƙasar

এছাড়াও পড়ুন:

Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS

Hukumar ƙididdigar a Najeriya NBS ta bayyana cewa an samu raguwar hauhawar farashin kaya a watan Agusta idan aka kwatanta da watan Yulin da ya gabace shi.

Cikin sabbin alƙaluman da NBS ta fitar a ranar Litinin sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.76 a watan Agustan saɓanin watan Yulin, wanda ya nuna karo na hudu ke nan a jere hauhawar farashin yana sauka.

NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna

Rahoton na hukumar NBS na zuwa ne kwanaki bayan da Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin karya farashin kayan abinci ƙasar.

A watanin baya-bayan an riƙa samun raguwar hauhawar farashin kayyaki a ƙasar.

Ko alƙaluman da NBS ta fitar a watan Yuni, ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka zuwa kashi 22.22 daga 22.97 da aka samu a watan Mayu.

A baya dai dai an yi ta kiraye-kirayen gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakan rage hauhawarar farashi domin magance tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya