HausaTv:
2025-08-01@10:41:41 GMT

Jagoran Kungiyar Ansarullah Ta Yemen Ya Shirin Na Tunkarar Harin Amurka

Published: 27th, January 2025 GMT

Jagoran kungiyar Ansarullah ya bayyana cewa: A shirye suke su tunkari duk wani harin Amurka kuma ya gargadin sojojin haya

Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyed Abdul-Malik Badruddeen al-Houthi ya tabbatar da cewa: Amurka ta yi amfani da dukkan karfinta wajen tallafawa haramtacciyar kasar Isra’ila da kuma kokarin murkushe al’ummar Falasdinu, yana mai jaddada tsayin daka da matsayarsa da ke tafiya a kan tubalin gaskiya, ikhlasi da ke gudana a tsakanin al’ummar Falastinu da ‘yan gwagwarmayarsu.

Sayyid Abdul-Malik Badruddeen al-Houthi ya bayyana a yayin zagayowar ranar shahadar Sayyid Hussein Badruddeen al-Houthi, cewa: Abin da hukumomi suka yi a shekara ta 2004 kan shahidi wanda shi ne ya kafa tattakin Alkur’ani, kuma shugaba shahidi Hussein Adwan, ba a yi adalci ba, yana mai nuni da cewa abin da shahidin Alkur’ani ya yi shi ne koyar da tarbiyyar Alkur’ani, da kalubalantar masu girman kai da kuma kauracewa kayayyakin Amurka da Haramtaciyyar kasar Isra’il kan matakin da suka dauka na kaddamar da hare-haren wuce gona kan al’ummar kasarsu.

Ya kara da cewa, bayan abubuwan da suka faru a ranar 11 ga watan Satumba, Amurka ta yi shirin mayar da ita tamkar wata kafa ta wani gagarumin yakin neman zabe na tsaurara iko a kan al’ummar kasar, da mamaye yankunanta da kuma kawar da asalinta, ya ci gaba da cewa gwamnatocin da suka mika wuya ga Amurka kuma an bude dukkan kofofin zuwa gare ta, ciki har da gwamnatin Yemen a karkashin taken kawancen yaki da ta’addanci, inda gwamnati a Yemen bayan a abubuwan da suka faru na ranar 11 ga watan Satumba suka bude hanya ga Amurka a cikin soja, tsaro, tattalin arziki, ilimi, kafofin watsa labaru da kuma maganganun addini.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka
  • Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan
  • Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana
  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta