Abin Fashewa Ya Hallaka Mutum Guda, Ya Jikkata 6 A Neja
Published: 27th, January 2025 GMT
Wani fashewa da ake zargin daga abubuwan fashewa ne da wani mai hakar zinariya ya ajiye a Sabon Pegi, ƙaramar hukumar Mashegu a Jihar Neja, ya yi sanadiyyar mutuwar mutum guda da jikkatar mutane shida a ranar Lahadi.
Rahotanni sun nuna cewa Yushau, wani mai haƙar haƙar zinariya, ya ajiye abubuwan fashewar ne a gida kafin su tashi yayin da ake shirya su don kai wa wuraren haƙar ma’adinai a yankin.
Kakakin Rundunar ’Yansanda ta Jihar Neja, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa fashewar ta yi sanadiyyar mutuwar Fatima Sadauki tare da jikkatar wasu mutane shida da aka kai Asibitin Kainji domin jinya. Haka kuma, gidaje 12 sun lalace sakamakon fashewar.
Kakakin ya ƙara da cewa kwamishinan ’yan sanda na jihar, Shawulu Ebenezer Danmamman, ya umurci a gudanar da bincike tare da tura tawaga ta cire abubuwan fashewa (EOD-CBRN) zuwa wurin domin bincike na musamman. Ya kuma bayyana cewa wanda ya ajiye abubuwan fashewar, Yushau tuni ya tsere, amma an tabbatar da zaman lafiya a yankin yayin da ake ci gaba da sa ido.
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
Manajar ofishin na NIWA, da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.
Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.
“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.
“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.
Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA, Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa da ke a sassan kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA