Abin Fashewa Ya Hallaka Mutum Guda, Ya Jikkata 6 A Neja
Published: 27th, January 2025 GMT
Wani fashewa da ake zargin daga abubuwan fashewa ne da wani mai hakar zinariya ya ajiye a Sabon Pegi, ƙaramar hukumar Mashegu a Jihar Neja, ya yi sanadiyyar mutuwar mutum guda da jikkatar mutane shida a ranar Lahadi.
Rahotanni sun nuna cewa Yushau, wani mai haƙar haƙar zinariya, ya ajiye abubuwan fashewar ne a gida kafin su tashi yayin da ake shirya su don kai wa wuraren haƙar ma’adinai a yankin.
Kakakin Rundunar ’Yansanda ta Jihar Neja, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa fashewar ta yi sanadiyyar mutuwar Fatima Sadauki tare da jikkatar wasu mutane shida da aka kai Asibitin Kainji domin jinya. Haka kuma, gidaje 12 sun lalace sakamakon fashewar.
Kakakin ya ƙara da cewa kwamishinan ’yan sanda na jihar, Shawulu Ebenezer Danmamman, ya umurci a gudanar da bincike tare da tura tawaga ta cire abubuwan fashewa (EOD-CBRN) zuwa wurin domin bincike na musamman. Ya kuma bayyana cewa wanda ya ajiye abubuwan fashewar, Yushau tuni ya tsere, amma an tabbatar da zaman lafiya a yankin yayin da ake ci gaba da sa ido.
এছাড়াও পড়ুন:
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
Aƙalla mutum 26 ne suka rasu sakamakon wasu sabbin hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka a Jihar Binuwai.
Hare-haren sun faru ne a yankunan Ƙaramar Hukumar Makurdi da Katsina-Ala tsakanin ƙarfe 12 na dare zuwa 2 na daren ranar Alhamis.
Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasuA Ƙaramar Hukumar Makurdi, wasu ’yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Mtswenem da Akondotyough Bawa, inda suka kashe mutum 25.
Haka kuma, an kashe mutum ɗaya a wani hari daban da aka kai ƙauyukan Kenvanger da Agbami a Ƙaramar Hukumar Katsina-Ala.
Wasu mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun shiga gidajen mutane suna harbin su yayin da suke barci, suna amfani da bindigogi da adduna.
Wani wanda ya tsira mai suna Iorpuu, ya ce mata da yara suna cikin waɗanda aka kashe, kuma har yanzu ana neman wasu da suka ɓace.
Ya ƙara da cewa wasu sun mutu ne a kan hanyarsu ta zuwa asibiti.
Wani ganau ya ce an fara kai harin ne wani ƙauye kusa da Jami’ar Noma da Fasaha ta Makurdi, inda aka kashe mutane huɗu.
Daga nan suka wuce wani ƙauye a kusa da unguwar Low Cost suka ci gaba da kashe mutane har adadin gawarwakin ya kai 25.
A Katsina-Ala, ’yan bindigar sun kai hari ƙauyukan Kenvanger da Agbami da misalin ƙarfe 1 na dare.
An ce sun yi yunƙurin yi wa wasu matan da suka haihu fyaɗe, amma mazan ƙauyen suka kai musu ɗauki.
Wannan ya haifar da rikici inda ’yan bindigar suka buɗe wuta, suka kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu.
A ƙauyen Agbami kuma, sun yi wa mutane da yawa dukan kawo wuƙa amma babu wanda ya mutu.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Udeme Edet, ya tabbatar da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya faru a Makurdi.
Ya ce za su ci gaba da bai wa ’yan jarida bayanai, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani.