Aminiya:
2025-11-03@00:56:31 GMT

Benfica ta naɗa Jose Mourinho sabon kociyanta

Published: 19th, September 2025 GMT

Benfica ta sanar da naɗa José Mourinho a matsayin sabon kociyanta, domin maye gurbin Bruno Lage, wanda ƙungiyar ta karo bayan da Qarabag ta doke ta a gasar Zakarun Turai ranar Talata.

Benfica ta kori Lage duk da cewa wasa ɗaya kawai ya yi rashin nasara a dukkanin gasa a bana.

Wata sanarwa da Benfica ta fitar a ranar Alhamis ta bayyana cewa, Mourinho mai shekaru 62 zai jagoranci ƙungiyar har zuwa kakar wasanni ta 2026/2027, tare da zaɓin raba gari a ƙarshen kakar nan.

An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar

Tsohon kociyan Chelsea, Real Madrid da Manchester United, ya dawo Benfica ne bayan ya rasa aiki a watan Agusta, wata ɗaya bayan da Fenerbahce ta kore shi sakamakon rashin samun gurbin Gasar Zakarun Turai.

Mourinho ya fara aiki a matsayin koci a Benfica a shekarar 2000, amma ya bar aiki bayan wasanni 11 kacal saboda saɓani da shugabanninta, lamarin da ya ba shi damar koma wa Porto, ƙungiyar da ya daukarwa kofin Zakarun Turai a 2004.

Tun da ya bar Benfica shekaru 25 da suka gabata, Mourinho ya yi aiki da manyan ƙungiyoyi kamar Chelsea, Inter Milan, Real Madrid, Tottenham, Roma da kuma Fenerbahce.

Ya lashe kofin Firimiyar Ingila guda uku, da La Liga, da Serie A, da Champions League guda biyu.

Sai dai daga 2017 zuwa yanzu, babban kambin da ya samu shi ne wanda ya lashe na Gasar Conference League da Roma a shekarar 2022.

A halin yanzu, Benfica tana matsayi na shida a teburin babbar gasar Portugal —Primeira Liga— da tazarar maki biyar tsakaninta da Porto, amma da kwantan wasa ɗaya.

Wasa na farko da Mourinho zai ja ragamar ƙungiyar da ke birnin Lisbon shi ne na ranar Asabar mai zuwa da AVS.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

 

Bayan an mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, kasashen duniya sun soma zura ido kan kasar Sin. Ana sa ran cewa, taron APEC da za a gudanar a Shenzhen, zai kara habaka hadin gwiwa, da samun ci gaba, da wadata tare a shiyyar, kana zai shaida yadda kasar Sin ke kara samar da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik, bisa ga sabbin nasarorin da take samu ta hanyar zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu November 2, 2025 Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa