Trump ya buƙaci ƙasashen NATO su daina cinikin man fetur da Rasha
Published: 14th, September 2025 GMT
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya buƙaci ƙasashen da ke cikin ƙungiyar tsaro ta NATO da su dakatar da cinikin mai da Rasha tare da sanya takunkumi, kafin Amurka ita ma ta bi sahu da irin nata takunkuman.
Trump ya wallafa wannan bayani a shafinsa na Truth Social, wanda ya bayyana a matsayin wasiƙa ga dukkanin mambobin NATO da ma duniya baki ɗaya.
Shugaban Amurkan ya ce ƙasarsa a shirye take ta sanya gagarumin takunkumi ga Rasha kan yaƙinta da Ukraine muddin ƙasashen NATO suka fara sanya irin nasu takunkumin da kuma dakatar da sayen mai na ƙasar.
“A shirye nake da in sanya manyan takunkumi kan Rasha, muddin dukkan ƙasashen NATO suka amince, kuma suka fara ɗaukar irin wannan mataki, da kuma lokacin da dukkan ƙasashen NATO suka daina sayen man fetur daga Rasha.”
Baya ga haka, Trump ya buƙaci mambobin ƙungiyar ƙasashen da ke yankin tekun Atlantika, su yi la’akari da ɗora harajin kashi 50 zuwa kashi 100 a kan China, a matsayin hanyar da za ta taimaka wajen kawo ƙarshen yaƙin Rasha a Ukraine.
Trump ya sha yi wa Rasha barazanar ƙarin takunkumi — ciki har da wanda ya sanar a ƙarshen makon da ya gabata bayan da Kremlin ta ƙaddamar da hare-hare ta sama mafi girma a kan Ukraine, amma har yanzu bai ɗauki wani mataki ba, lamarin da ke fusata Kyiv.
Shugaban wanda ya gana da takwaransa na Rasha Vladimir Putin a watan da ya gabata a wani taro a Alaska, ya bayyana sayen man fetur na Rasha da ƙasashen NATO ke yi a matsayin abin mamaki, ya kuma ce hakan yana raunana ƙarfin gogayyar kasuwancinsu da Moscow.
Trump ya ce, muddin ƙawancen ƙasashen mai mambobi 32 suka ɗauki shawararsa, to lallai wannan yaƙi zai ƙare cikin ƙanƙanin lokaci, amma kuma idan ba haka ba, to suna ɓata lokaci ne kawai.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar
“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.
Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp