Aminiya:
2025-11-02@17:03:42 GMT

Mun kori Falasɗinawa sama da dubu 250 daga Gaza — Isra’ila

Published: 14th, September 2025 GMT

Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta yi nasarar korar Falasɗinawa sama da mutum 250,000 daga birnin Gaza tun bayan da suka fara zafafa kai hare-hare a yankin.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da jami’an Falasɗinu suka ce da dama sun gaza ficewa daga kudancin ƙasar saboda cunkoso.

Najeriya ta daɗe tana fama da shugabanni marasa nagarta — Sanusi II ’Yan rakiyar amarya 19 sun mutu a hatsarin mota a Zamfara

Mai magana da yawun sojojin Avichay Adraeeya wallafa haka a shafin X, yana cewa fiye da kashi 1 bisa huɗu na waɗanda suka rage a Gaza sun gujewa birnin don kare lafiyarsu.

Sai dai, Hukumar Tsaron Farar Hula ta Gaza, ta ba da rahoton cewa adaɗin waɗanda suka samu nasarar tsarewa bai wuce mutum dubu 70 ba.

Daƙile kafofin yada labarai a Gaza da matsalolin shiga yankunan ya sa AFP ba ta iya tabbatar da bayanan da sojoji ko kuma na tsaron farar hula suka bayar ba.

A jiya Asabar ce sjojin Isra’ila sun jefa wasu takardu zuwa birnin suna kira ga mazauna yankunan yammacin ƙasar da su yi ƙaura, yayin da jami’an tsaron farar hula suka ba da rahoton cewa Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare ta sama.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi ƙiyasta cewa, a ƙarshen watan Agusta kimanin Falasɗinawa miliyan ɗaya ne ke zaune a cikin birnin Gaza da kewayen, inda ta ce ana fama da yunwa bayan da aka kwashe watanni ana fama da munanan yanayi.

MDD da wasu manyan ƙasashen sun buƙaci sojojin da su yi watsi da shirinsu na ƙwace birnin, suna masu gargaɗin bubu abin da hakan zai haifar face sake tsananta al’amuran jinƙai a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

 

Gwamnatin Jihar Kwara ta kafa kwamitoci biyu domin tantance bayanan wadanda suka yi  ritaya a matakin jiha da  kananan hukumomi.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinar Kudi ta jihar, Dakta Hauwa Nuru ta fitar, ta bayyana cewa kwamitocin za su tantance tare da tabbatar da sahihancin bayanan wadanda suka yi ritaya, domin a biya su bisa lokacin da suka bar aikin gwamnati.

A cewarta, kwamitin mutum takwas da aka kafa don kula da kudaden ritaya na matakin jiha zai kasance karkashin jagorancin Mai Duba Asusun Jiha, wato (Auditor General), yayin da wanda ke kula da matakin kananan hukumomi zai kasance karkashin Mai Duba Asusun Kananan Hukumomi.

Sanarwar ta bayyana cewa babban burin kwamitocin shi ne tabbatar da cewa an tattara bayanan masu ritaya bisa gaskiya da adalci, tare da  biyan su kai tsaye ta asusun ajiyar banki.

Ta kara da cewa, mambobin kwamitocin sun hada da wakilan tsofaffin manyan sakatarorin, kungiyar tsofaffin ma’aikata, Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), da kungiyar kwadago ta TUC, da sauransu.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu