Aminiya:
2025-09-17@20:28:15 GMT

Mun kori Falasɗinawa sama da dubu 250 daga Gaza — Isra’ila

Published: 14th, September 2025 GMT

Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta yi nasarar korar Falasɗinawa sama da mutum 250,000 daga birnin Gaza tun bayan da suka fara zafafa kai hare-hare a yankin.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da jami’an Falasɗinu suka ce da dama sun gaza ficewa daga kudancin ƙasar saboda cunkoso.

Najeriya ta daɗe tana fama da shugabanni marasa nagarta — Sanusi II ’Yan rakiyar amarya 19 sun mutu a hatsarin mota a Zamfara

Mai magana da yawun sojojin Avichay Adraeeya wallafa haka a shafin X, yana cewa fiye da kashi 1 bisa huɗu na waɗanda suka rage a Gaza sun gujewa birnin don kare lafiyarsu.

Sai dai, Hukumar Tsaron Farar Hula ta Gaza, ta ba da rahoton cewa adaɗin waɗanda suka samu nasarar tsarewa bai wuce mutum dubu 70 ba.

Daƙile kafofin yada labarai a Gaza da matsalolin shiga yankunan ya sa AFP ba ta iya tabbatar da bayanan da sojoji ko kuma na tsaron farar hula suka bayar ba.

A jiya Asabar ce sjojin Isra’ila sun jefa wasu takardu zuwa birnin suna kira ga mazauna yankunan yammacin ƙasar da su yi ƙaura, yayin da jami’an tsaron farar hula suka ba da rahoton cewa Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare ta sama.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi ƙiyasta cewa, a ƙarshen watan Agusta kimanin Falasɗinawa miliyan ɗaya ne ke zaune a cikin birnin Gaza da kewayen, inda ta ce ana fama da yunwa bayan da aka kwashe watanni ana fama da munanan yanayi.

MDD da wasu manyan ƙasashen sun buƙaci sojojin da su yi watsi da shirinsu na ƙwace birnin, suna masu gargaɗin bubu abin da hakan zai haifar face sake tsananta al’amuran jinƙai a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.

 

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.

 

Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza.
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa