Likitoci sun bai wa gwamnati sa’o’i 24 kafin tsunduma yajin aiki
Published: 11th, September 2025 GMT
Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Sanin Makamar Aiki ta Najeriya (NARD), ta bai wa Gwamnatin Tarayya sa’o’i 24 don ɗaukar mataki game da buƙatunsu, ko kuma su tsunduma yajin aiki.
Wannan matakin ya biyo bayan cikar wa’adin gargaɗin kwanaki 10 da suka bayar a baya.
Gwamnatin Tarayya za ta gurfanar da shugabannin Ansaru 2 a kotu Tinubu ya bayar da umarnin a sake karya farashin kayan abinciTuni wasu likitoci a Abuja da Jihar Oyo suka tsunduma yajin aiki.
Likitocin, waɗanda yawancinsu ke aiki a Asibitocin Koyarwa da na Ƙwararru, suna yawan tafiya yajin aiki saboda rashin biyan wasu haƙƙoƙinsu.
A halin yanzu, suna neman a biya su kuɗin horon 2025 da bashin albashin da suka bi, sannan sun buƙaci a hanzarta biyansu wani kuɗaɗen alawus-alawus.
Hakazalika, sun buƙaci gwamnati ta amince da takardar shaidar digiri ta ‘West African postgraduate’, sannan a magance matsalolin da suka shafi walwalarsu a Jihar Kaduna da kuma Asibitin Koyarwa na LAUTECH, da ke Ogbomoso.
Shugaban NARD, Dokta Tope Osundara, ya ce wannan mataki da suka ɗauka ya biyo bayan taron awanni shida na kwamitin gudanarwa na ƙasa da suka gudanar ta Intanet.
Ya ƙara da cewa gwamnatin ta yi alƙawarin ɗaukar mataki game da buƙatunsu amma dole ne a hanzarta aiwatar da su.
Ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ba ta yi wani abu a kan buƙatun nasu ba, za su fara yajin aiki a ranar Juma’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya wa adi Yajin aiki
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’uSauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.
An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.
Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.
Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.
Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.