Aminiya:
2025-09-17@21:49:42 GMT

Sarkin Zazzau ya jagoranci jama’a domin murnar Maulidin bana

Published: 5th, September 2025 GMT

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya jagoranci jerin gwanon zuwa gidan Sarkin Ladanai na Zazzau a matsayin al’adar tarihi na bikin Mauludin na bana.

Bikin Mauludin na bana shi ne karo na 185 da aka shirya a hukumance da aka gudanar a Zariya.

An kama mace ɗauke da bindiga da N2m a otal Mauludi: ’Yan sanda sun haramta hawa babur da daddare a Gombe

Sarkin da ya hau kan doki ya samu rakiyar ’yan uwa na masarautar domin yin mubaya’a ga fitaccen gidan malamin addinin Musulunci, wato gidan Sarkin Ladanai.

An gudanar da bukukuwan murnar ne  don zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

Manyan Malaman Addinin Musulunci sun gudanar da addu’o’i a harabar domin samar da tsaro da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Masarautar Zazzau da ke Jihar Kaduna da Najeriya baki ɗaya.

Abu Ladan, Sarkin Ladanai na farko da ya koyar da ilimin addinin Musulunci a makarantar da mahaifinsa Kanuri ya kafa a lokacin da ya tafi aikin hajji da ƙafa ya dawo da wasu littattafai.

Ana karanta waɗannan littafai na Musulunci a gidan duk ranar 12 ga watan Rabi’ul Awwal a matsayin wani ɓangare na tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (S.A.W).

Waɗannan sun haɗa da yin salati ga annabi da addu’o’in zaman lafiya da wadata da ci gaban al’ummar Zazzau.

Tun daga wannan lokacin har zuwa yau, ana ci gaba da karatu da yin addu’o’in Maulidin Annabi a gidan Sarkin Ladanai.

Sarkin Zazzau, tun daga wancan zamani zuwa yanzu, ya ci gaba da halartar taron na shekara-shekara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mai Martaba Sarkin Zazzau Sarkin Ladanai

এছাড়াও পড়ুন:

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

A yau Laraba ne aka bude bikin baje koli karo na 22, na Sin da kasashe membobin kungiyar ASEAN ko (CAEXPO), da kuma taron dandalin kasuwanci da juba jari na Sin da ASEAN ko CABIS, a birnin Nanning na jihar Guangxi ta kabilar Zhuang mai cin gashin kai dake kudancin kasar Sin.

A shekarun baya bayan nan, Sin da kungiyar ASEAN, sun ci gaba da cimma manyan nasarori tare a fannin bunkasa dunkulewar tattalin arzikin shiyyarsu, da fadada damar bai daya ta cudanyar mabambantan sassa, a gabar da ake fuskantar yanayin tangal-tangal a duniya.

Wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ta shaida yadda kaso 92.8 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyi suka amince cewa, baje kolin CAEXPO ya bayyana yadda Sin da kungiyar ASEAN suka himmatu wajen bunkasa bude kofa bisa matsayin koli, da kare tsarin cinikayya cikin ’yanci da kasancewar mabambantan sassa.

Kafar CGTN ta gabatar da kuri’ar ne da harsunan Turanci, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da yaren Rasha, inda kuma mutane 6,260 suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’ao’i 24. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin