Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau
Published: 3rd, September 2025 GMT
Tarihi ya yi mana gargadi da cewa, makomar dan adam tana hade da juna, kuma kowace kasa, da kowace kabila dole ne su daidaita da juna, su zauna lafiya, su taimaki juna, domin ta haka ne kawai za a iya kiyaye tsaro na gama gari, da kawar da tushen yaki, da tabbatar da tarihi bai maimaita kansa ba!
A jawabin nasa, shugaba Xi ya bayyana cewa, al’ummar kasar Sin babbar al’umma ce mai dogaro da kanta, wadda ba ta jin tsoron masu nuna karfin tuwo.
A yau, dan Adam na fuskantar zabi na zaman lafiya ko yaki, da tattaunawa ko nuna adawa, da samun nasara tare ko kin hadin gwiwa. Jama’ar kasar Sin suna tsayawa tsayin daka kan gaskiya da ci gaban wayewar kan dan Adam, tare da bin hanyar ci gaba cikin lumana, kuma suna aiki tare da jama’ar kasa da kasa don gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya.
Ya ce ya wajaba daukacin dakarun sojojin kasar su gudanar da ayyukansu bisa gaskiya, su hanzarta gina rundunar sojoji ta zamani, tare da nacewa kare ’yancin kan kasar Sin, da hadin kai da kare kimar yankunan kasar.
Kazalika, shugaba Xi ya yi kira ga daukacin dakarun sojojin kasar da su samar da tsare-tsare na farfadowa da daukacin kasar Sin bisa babban matsayi, tare da bayar da gagarumar gudummawa wanzar da zaman lafiya da ci gaban duniya. (Bilkisu Xin, Amina Xu, Safiyah Ma, Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Duk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa.
Wannan matsala ta daɗe tana jawo muhawara tsakanin iyaye, malamai da hukumomin ilimi.
Wasu na ganin matsaloli ne da ba za su rasa nasaba da rashin kulawa da watsi da harkar ilimi da gwamnati ta yi ba.
Ko wadanne dalilai ne suka daliban makarantun masu zaman kansu suka fi kokari idan aka kwatanta da daliban makarantu na gwamnati?
NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyyaWannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan