Amurka ta hana izinin shiga kasarta ga shugaban Falastinawa don halartar taron MDD
Published: 30th, August 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta sanar a jiya Juma’a cewa, sakataren harkokin wajen kasar Marco Rubio ya yanke shawarar soke takardar izinin shiga kasar ga wasu mambobin kungiyar ‘yantar da ‘yancin Falasdinu (PLO) da hukumar Falasdinu (PA), ciki har da shugaban PA Mahmoud Abbas, gabanin taron shekara-shekara na Majalisar Dinkin Duniya da za a yi a birnin New York na watan Satumba mai zuwa.
Wadannan matakai na nufin cewa da alama Abbas ba zai iya zuwa New York don gabatar da jawabinsa na shekara kamar yadda ya saba yi ba.
Wannan mataki dai na cikin jerin takunkuman da Amurka ta kakabawa jami’an Falasdinawa a watan Yulin da ya gabata, a daidai lokacin da wasu kasashen yammacin duniya ke neman amincewa da kasar Falasdinu a hukumance.
A cewar sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar, wadannan takunkumin ba su hada da aikin hukumar Falasdinu a Majalisar Dinkin Duniya ba, kuma ma’aikatar ba ta bayar da wani karin bayan ikan hakan ba.
Sai dai fadar shugaban kasar Falasdinu ta bayyana matukar mamakinta game da matakin na Amurka, inda ta jaddada cewa ya sabawa dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar MDD, musamman ganin cewa Falasdinu mamaba ce mai sa ido a MDD.
Ta yi kira ga gwamnatin Amurka da ta sake nazari tare da janye shawarar da ta yanke, tare da tabbatar da kudurinta na bin dokokin kasa da kasa.
Ma’aikatar harkokin wajen Falasdinu ta bayyana hakan a matsayin yin fatali da kudurorin MDD da aka rattaba a hannu a kansu a cikin yarjejeniyar 1947.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rwanda ta dauki bakin haure kashi na farko da aka kora daga Amurka August 30, 2025 Jami’in Sojin Isra’ila: Masu Tunanin Hizbullah Ta Yi Rauni Suna Mafarki Ne August 30, 2025 Mali: Kungiyar Al-Qaeda ta kwace iko da garin Farabougou da ke tsakiyar kasar August 30, 2025 Mutum Guda Ya Yi Shahada Sanadiyar Harin Isra’ila A Kudancin Lebanon August 29, 2025 Malasiya Ta Bukaci A Kori Isara’ila (HKI) Daga MDD August 29, 2025 Iran: China Ta Zuba Jari A Aikin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana A Bushar August 29, 2025 MDD Ta Yi Tir Da Dirar Mikiyan Da Jamus Takewa Masu Goyon Bayan Falasdinawa August 29, 2025 Majalisar dokokin Iran ta gabatar da kudirin ficewa daga NPT August 29, 2025 Guterres: Dole ne a kawo karshen halin da ake ciki a Gaza August 29, 2025 Pezeshkian: Alakar Iran, China Na Da Amfani Mai Yawa Ga Kasashen Biyu August 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
Babban sakataren majalisar koli ta tsaron jamhuriyar musulunci ta Iran Dr. Ali Larijani ya bayyana cewa; Za a bunkasa aiki tare a tsakanin Iran da Saudiyya a fagagen tattalin arziki da kuma tsaro.
Dr. Larijani ya bayyana hakan ne jim kadan bayan fitowar daga ganawar da ya yi da Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mu8hammad Bin Salman.
Bugu da kari Dr. Ali Larijani ya ce a yayin ganawarwa da Yarima mai jiran gado na Saudiyya Muhammad Bin Salman, sun tattauna hanyoyin bunkasa alakar kasashensu ta fuskoki mabanbanta, da kara girman wannan alakar ta fuskar tattalin arzki da tsaro fiye da yadda take a yanzu.”
Haka nan kuma ya ce, za a yi aiki domin kawar da dukkanin abubuwan da suke kawo cikas a kan hanyar bunkasa wannan alakokin.
Dr. Ali Larijani ya kuma ce,an yi shawara akan yadda kasashen yankin za su bunkasa alakarsu ta tsaro domin ganin an tabbatar da zaman lafiya.
Da aka tambaye shi akan ko an sami sauyi akan mahangar kasashen Larabawa bayan harin da HKI ta kai wa Qatar, Dr.Ali Larijani ya ce; Tabbas da akwai sauyi a cikin yadda kasashen larabawa suke Kallon abubuwan da suke faruwa, domin suna ganin cewa kasantuwar HKI a cikin wannan yankin yana hana zaman lafiya.
Babban sakataren Majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya ziyarci Saudiyya inda ya gana da ministan tsaronta da kuma Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar Kasuwanci Da HKI September 17, 2025 Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Gaza September 17, 2025 Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila September 17, 2025 Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta September 17, 2025 Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci